< Luka 9 >

1 Sklicavši pa dvanajstere učence svoje, dá jim moč in oblast nad vsemi hudiči, in da naj uzdravljajo bolezni;
Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
2 In odpošlje jih oznanjevat kraljestva Božjega, in uzdravljat bolnike.
Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 In reče jim: Ničesar ne jemljite na pot; ne palice, ne torbe, ne kruha, ne denarja; tudi po dva plašča ne imejte.
Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
4 In v kterokoli hišo vnidete, tu prebivajte, in odtod izhajajte.
Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
5 In kterikoli vas ne sprejmó, izidite iz tistega mesta, in otresite prag z nog svojih, za pričo zoper njih.
Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
6 Ter izidejo in hodili so po vaséh, oznanjujoč evangelj in uzdravljajoč povsodi.
Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
7 Slišal je pa Herod četrtnik vse, kaj on dela; in ni se mogel načuditi, ker so nekteri pravili: Janez je vstal od mrtvih;
Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
8 A drugi: Elija je prišel; drugi pa: Starih prerokov eden jo vstal.
Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
9 Pa reče Herod: Janeza sem jaz posekal; kdo pa je ta, za kogar jaz slišim takošne reči? In želel ga je videti.
Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
10 In vrnivši se aposteljni, povedó mu, kar so storili; in vzeme jih, in odide posebej na samoten kraj mesta, ktero se imenuje Betsajda.
Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
11 Zvedevši pa to ljudstvo, odidejo za njim; in sprejme jih, in govoril jim je o kraljestvu Božjem, in kteri so potrebovali zdravja, uzdravljal jih je.
Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
12 A dan se je jel nagibati; in pristopivši dvanajsteri, rekó mu: Odpusti ljudstvo, da odidejo v okolne vasi in pristave, in tam prenočé, in najdejo živeža: kajti tu smo v samotnem kraji.
Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
13 Pa jim reče: Dajte jim vi jesti. Oni pa rekó: Nimamo več, nego pet hlebov in dve ribi, razen če odidemo mi, da kupimo za vse to ljudstvo jedî.
Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
14 Bilo jih je namreč kakih pet tisoči mož. Pa reče učencem svojim: Posadite jih po petdeset v vrsto.
Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
15 In storé tako, in posadé vse.
Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
16 Vzemši pa petere hlebe in tisti dve ribi, ozrè se na nebo in jih blagoslovi, ter prelomi, in dajal je učencem, naj položé pred ljudstvo.
Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
17 In jedli so, in nasitili so se vsi; in pobrali so, kar jim je ostalo od košcev, dvanajst košev.
Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
18 In zgodí se, ko je na samem molil, bili so ž njim učenci; in vpraševal jih je, govoreč: Kdo pravijo ljudjé, da sem jaz?
Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
19 Oni pa odgovarjajoč, rekó: Janez Krstnik; drugi pa Elija; a drugi, da je eden starih prerokov vstal.
Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
20 Pa jim reče: Vi pa, kdo pravite, da sem jaz? Odgovarjajoč pa Peter, reče: Kristus Božji.
Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
21 A on jim zapretí in naročí, naj nikomur ne povedó tega,
Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
22 Govoreč: Sinu človečjemu je treba veliko pretrpeti, in zavrženemu biti od starešin in vélikih duhovnov in pismarjev, in umorjenemu biti, in tretji dan vstati.
Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
23 In pravil je vsem: Če kdo hoče za menoj iti, zatají naj samega sebe, in vzeme križ svoj vsak dan, in gre za menoj.
Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
24 Kajti kdor hoče dušo svojo ohraniti, izgubil jo bo; kdor pa izgubí dušo svojo za voljo mene, ta jo bo ohranil.
Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
25 Kaj namreč pomaga človeku, če pridobí ves svet, samega sebe pa pogubí ali si škodo napravi?
Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
26 Kdor se bo namreč sramoval mene in mojih besed, tega se bo tudi sin človečji sramoval, kedar pride v svojej in očetovej in svetih angeljev slavi.
Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
27 Pravim vam pa resnično, da so nekteri med témi, ki stojé tu, kteri ne bodo okusili smrti, dokler ne vidijo kraljestva Božjega.
Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
28 Zgodí se pa kakih osem dní po teh besedah, pa vzeme Petra in Jakoba in Janeza, in izide na goro molit.
Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
29 In ko je molil, postane podoba obličja njegovega drugačna, in oblačilo njegovo belo in svetlo.
Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
30 In glej, moža dva sta govorila ž njim, ktera sta bila Mojzes in Elija;
Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
31 Ktera sta se prikazala v slavi in sta govorila o koncu njegovem, ki ga je imel dokončati v Jeruzalemu.
Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
32 A Peter in ktera sta bila ž njim, bili so zaspali; a ko se prebudé, ugledajo slavo njegovo, in oba moža, ktera sta ž njim stala.
Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
33 In zgodí se, ko sta odhajala od njega, reče Peter Jezusu: Učenik, dobro nam je tu biti; bomo pa naredili tri šatore, enega tebi, in Mojzesu enega, in enega Eliju: ne vedoč, kaj govori.
Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
34 Ko je pa to govoril, nastane oblak in ju zakrije; in zbojé se, ko vnideta v oblak.
Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
35 In glas se oglasí iz oblaka, govoreč: Ta je sin moj ljubljeni; njega poslušajte.
Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
36 In ko se je bil glas oglasil, najdejo Jezusa samega. In oni zamolčé, in nikomur niso tiste dní nič povedali od tega, kar so bili videli.
Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
37 Zgodí se pa drugi dan, ko pridejo z gore, sreča ga veliko ljudstva.
Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
38 In glej, mož iz ljudstva zavpije, govoreč: Učenik, prosim te, ozri se na sina mojega; kajti edinec mi je.
Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
39 In glej, hudič ga napada, in precej kričí, in lomi ga s peno, in komaj potem odide od njega, ko ga je zvil.
Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
40 In prosil sem učence tvoje, naj bi ga izgnali, in niso mogli.
Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
41 Odgovarjajoč pa Jezus, reče: O rod neverni in popačeni! doklej bom pri vas in vas bom trpel? pripelji sèm sina svojega!
Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
42 In ko je še k njemu šel, zgrabi ga hudič in strese; a Jezus zapretí duhu nečistemu, in uzdravi dečka, in dá ga očetu njegovemu.
Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
43 In vsi so se čudili veličastvu Božjemu. Ko so se pa vsi čudili vsemu, kar je storil Jezus, reče učencem svojim:
Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
44 Ohranite vi v ušesih svojih te besede; kajti sin človečji bo izdan v roke človeške.
“Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
45 Oni pa niso umeli te besede, in bila jim je prikrita, da je niso razumeli; in bali so se, da bi ga vprašali za to besedo.
Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
46 Všla je bila pa misel vanje, kdo bi bil največi med njimi.
Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
47 Jezus pa, vedoč misel srca njih, vzeme otroka, in postavi ga pred se,
Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
48 In reče jim: Kdorkoli sprejme tega otroka v ime moje, mene sprejema; a kdorkoli mene sprejme, sprejema tega, kdor me je poslal. Kdor je namreč najmanji med vami, ta bo velik.
sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
49 Odgovarjajoč pa Janez, reče: Učenik, videli smo nekoga, kteri je z imenom tvojim izganjal hudiče; in zabranili smo mu, ker ne hodi z nami za teboj.
Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
50 In reče mu Jezus: Ne branite! Kdor namreč ni zoper nas, on je z nami.
Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
51 Zgodí se pa, ko so se dopolnjevali dnevi vzhoda njegovega, pa se on na ravnost v Jeruzalem nameri.
Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
52 In pošlje poslance pred obličjem svojim; in ti odidejo in vnidejo v vas Samarijansko, da mu pripravijo prenočišča.
Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
53 Ali niso ga hoteli sprejeti, ker so videli, da gre v Jeruzalem.
Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
54 Videvši pa to učenca njegova Jakob in Janez, rečeta: Gospod, hočeš li, da rečeva, naj ogenj snide z neba, in jih potrebi, kakor je tudi Elija storil?
Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
55 Obrnivši se pa, zapretí jim, in reče: Ne véste, kakošnega duha ste vi;
Amma, ya juya ya tsauta masu.
56 Sin človečji namreč ni prišel duš človeških gubit, nego da jih zveliča, In šli so v drugo vas.
Sai suka tafi wani kauye dabam.
57 Zgodí se pa, ko so šli, reče mu nekdo po poti: Šel bom za teboj, karmorkoli odideš, Gospod!
Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
58 In reče mu Jezus: Lisice imajo brloge, in tice nebeške gnezda; a sin človečji nima kje glave nasloniti,
Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
59 A drugemu reče: Pojdi za menoj! On pa reče: Gospod, dovoli mi, da prej odidem in pokopljem očeta svojega.
Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
60 Ali Jezus mu reče: Pusti, naj mrliči pokopljejo mrliče svoje; ti pa pojdi in oznanjuj kraljestvo Božje.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
61 Zopet drugi pa reče: Šel bom za teboj, Gospod! ali dovoli mi, da se poprej poslovim z domačimi svojimi.
Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
62 In reče mu Jezus: Nobeden ni pripraven za kraljestvo Božje, kdor položí roko svojo na plug, pa se ozira na to, kar je zadej.
Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”

< Luka 9 >