< Luka 17 >

1 Reče pa učencem svojim: Ni mogoče, da pohujšanja ne bi prišla; ali gorjé tistemu, po kterem prihajajo.
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 Bolje bi mu bilo, da bi mu se obesil kamen mlinski na vrat, ter bi bil vržen v morje, nego da enega teh malih pohujša.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Varujte se! Če se pregreší brat tvoj zoper tebe, popreti mu; in če se spokorí, odpusti mu.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 In če se pregreší sedemkrat na dan zoper tebe, pa se sedemkrat na dan obrne do tebe, govoreč: Kesam se! odpusti mu.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 Pa rekó aposteljni Gospodu: Priloži nam vere!
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 Gospod pa reče: Ako bi imeli vere, kolikoršno je zrno gorušično, in bi rekli tej murvi: Izderi se, in vsádi se v morje! in poslušala bi vas.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 Kdo izmed vas ima pa hlapca, kteri orje in pase, da bi mu, kedar pride s polja, precej rekel: Pojdi, počij?
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 Ne poreče li mu marveč: Pripravi, kar bom večerjal, in opaši se in strezi mi, dokler se ne najém in napijem; a potem jej in pij ti?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Ali bo mar zahvalil temu hlapcu, da je storil, kar mu se je bilo ukazalo? Ne verujem.
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 Tako tudi vi, kedar storite, kar vam je ukazano, recite: Nepotrebni hlapci smo; kajti storili smo, kar smo bili dolžni storiti.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 In zgodí se, ko je šel v Jeruzalem, da je hodil med Samarijo in Galilejo.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 In ko vnide v neko vas, sreča ga deset gobavih móž, kteri so stali od daleč.
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 In ti povzdignejo glas, govoreč: Jezus, učenik, usmili se nas!
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 In ugledavši jih, reče jim: Pojdite, pokažite se duhovnom! In zgodí se, ko so šli, očistijo se.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 Eden pa izmed njih, videvši, da je ozdravel, vrne se, hvaleč Boga z močnim glasom;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 In pade na obraz pred noge njegove, in zahvali mu; in ta je bil Samarijan.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 Odgovarjajoč pa Jezus, reče: Ali se jih ni deset očistilo? Onih devet pa, kje so?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 Ali se ni našel, kteri bi se vrnil, da bi dal Bogu hvalo, razen ta tujec?
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 In reče mu: Vstani, pojdi! vera tvoja ti je pomogla.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Vprašan pa od Farizejev, kedaj bo prišlo kraljestvo Božje, odgovorí jim, in reče: Kraljestvo Božje ne bo prišlo s svetlostjo.
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Tudi ne porekó: Glej, tu je! ali: Glej, tam je! Kajti glej, kraljestvo Božje je notri v vas.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Reče pa učencem: Prišli bodo dnevi, ko boste želeli enega od dnî sinú človečjega videti, in ne boste videli.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 In porekó vam: Glej, tu je! ali: Glej, tam je! Ne izidite, in tudi ne sledite ne!
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Kajti kakor blisk, kteri šine in se svetli iz enega kraja pod nebom do drugega kraja pod nebom, tako bo tudi sin človečji v dan svoj.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 Ali poprej mu je treba veliko pretrpeti, in zavrženemu biti od tega rodú.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 In kakor je bilo v dnéh Noeta, tako bo tudi v dnéh sinu človečjega.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 Jedli so, pili so, ženili so se, možile so se, noter do dné, ko je stopil Noe v barko, ter je prišel potop in vse pogubil.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 Enako tudi, kakor je bilo v dnéh Lota; jedli so, pili so, kupovali so, prodajali so, sadili so, zidali so;
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 Ali tisti dan, ko je izšel Lot iz Sodome, udaril je ogenj in žveplo z neba, in pogubil je vse.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Ravno tako bo tisti dan, ko se bo sin človečji razodel.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 Tisti dan, kdor bo na strehi, a pohištvo njegovo v hiši, ne stopa naj dol, da ga vzeme; in kdor bo na polji, naj se ravno tako ne ozira na to, kar je zadej.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Spominjajte se žene Lotove!
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Kdor bo gledal dušo svojo ohraniti, izgubil jo bo; a kdor jo bo izgubil, oživil jo bo.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 Pravim vam: Tisto noč bosta dva na enej postelji: eden se bo vzel, a drugi pustil.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Dve boste mleli vkupej: ena se bo vzela, a druga pustila.
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 Dva bosta na njivi: eden se bo vzel, a drugi pustil.
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 In odgovarjajoč, rekó mu: Kje, Gospod? A on jim reče: Kjer je truplo, tam se bodo zbirali orli.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luka 17 >