< Luka 16 >

1 Pravil pa je tudi učencem svojim: Bil je en človek bogat, kteri je imel pristavnika; in tega so bili ovadili pri njem, da mu razsiplje imenje.
Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
2 In poklicavši ga, reče mu: Kaj to slišim za te? Daj račun od gospodarstva svojega, ker ne moreš dalje gospodariti.
Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
3 A pristavnik reče sam s seboj: Kaj bom storil, ko mi gospodar moj odjemlje gospodarstvo? Kopati ne morem, prositi me je sram.
Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
4 Vém, kaj bom storil, da me bodo, kedar bom odstavljen gospodarstva, sprejeli v hiše svoje.
Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5 In poklicavši vsakega posameznega od dolžnikov gospodarja svojega, reče prvemu: Koliko si dolžen gospodarju mojemu?
Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
6 On pa reče: Sto mer olja. In reče mu: Vzemi svojo pismo, pa sedí hitro, in napiši petdeset.
Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
7 Po tem reče drugemu: A ti koliko si dolžen? On pa reče: Sto korcev pšenice. In velí mu: Vzemi svoje pismo, in napiši osemdeset.
Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8 In gospodar pohvali krivičnega hlapca, da je pametno storil. Kajti sinovi tega sveta so pametniji od sinov svetlobe v svojem rodu. (aiōn g165)
Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
9 Tudi jaz vam pravim: Naredite si prijateljev s krivičnim bogastvom, da vas, kedar ubožate, sprejmó v večna stanovališča. (aiōnios g166)
Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
10 Kdor je v najmanjem zvest, zvest je tudi v velikem; in kdor je v najmanjem krivičen, krivičen je tudi v velikem.
Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
11 Če torej v krivičnem bogastvu niste bili zvesti, kdo vam bo zaupal pravično?
Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
12 In če v tujem niste bili zvesti, kdo vam bo dal, kar je vaše?
Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13 Noben hlapec ne more dvema gospodoma služiti: ali bo enega sovražil, in drugega ljubil; ali se bo enega držal, in drugega bo zaničeval. Ne morete Bogu služiti in mamonu.
Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
14 Poslušali so pa vse to tudi Farizeji, kteri so srebro ljubili, ter so ga zasmehovali.
Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
15 Pa jim reče: Vi ste tisti, kteri se delate pravične pred ljudmí; ali Bog pozná srca vaša: kajti kar je pri ljudéh visoko, gnjusoba je pred Bogom.
Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16 Zakon in preroki so do Janeza; odtlej se oznanjuje kraljestvo Božje, in vsak s silo va-nj tišči.
Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
17 Laže je pa nebu in zemlji prejti, nego enej pičici iz zakona izpasti.
Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18 Vsak, kdor pustí ženo svojo in se oženi z drugo, prešestvuje; in vsak, kdor popuščeno od moža vzeme, prešestvuje.
Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19 Bil je pa neki človek bogat, in oblačil se je v škrlat in tančico, in razveseljeval se je vsak dan sijajno.
Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
20 Bil je pa neki ubožec po imenu Lazar, kteri jo ležal pred vratmi njegovimi, gnôjen,
Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
21 In hrepeneč nasititi se z drobtinami, ktere so padale z mize bogatina; ali tudi psi so dohajali, ter so lizali gnoj njegov
Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22 Zgodí se pa, da ubožec umrè, in odnesó ga angelji na naročje Abrahamovo; umrè pa tudi bogatin, in pokopljejo ga.
Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
23 In v peklu, ko je bil v bolečinah, povzdigne očí svoje, in ugleda Abrahama od daleč, in Lazarja na naročji njegovem. (Hadēs g86)
yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
24 In on zaklicavši, reče: Oče Abraham! usmili se me, in pošlji Lazarja, naj omoči konec prsta svojega v vodi, in mi jezik ohladí, ker se mučim v tem plamenu.
Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25 Abraham pa reče: Sin! spomeni se, da si ti prejel dobroto svojo v življenji svojem, in ravno tako Lazar slabo. Sedaj pa; on se tolaži, a ti se mučiš.
Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 In vrh vsega tega, med nami in vami je postavljen prepad velik, da kteri hočejo odtod sniti k vam, ne morejo, in kteri odondod k nam, da ne prehajajo.
Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27 Pa reče: Prosim te torej, oče, da ga pošlji na mojega očeta dom,
Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
28 Ker imam pet bratov: da jim to izpriča, da ne pridejo tudi oni na ta kraj trpljenja.
domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29 Velí mu Abraham: Mojzesa imajo in preroke; poslušajo naj jih.
Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
30 On pa reče: Ne, oče Abraham! nego če kdo od mrtvih pride k njim, potem se bodo spokorili.
Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
31 Pa mu reče: Če Mojzesa in prerokov ne poslušajo, ne bodo verovali, če tudi kdo od mrtvih vstane.
Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”

< Luka 16 >