< Luka 10 >
1 Po tem pa izvoli Gospod še drugih sedemdeset, in pošlje jih po dva in dva pred obličjem svojim v vsako mesto in kraj, kamor je imel sam priti.
Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
2 In pravil jim je: Žetve je sicer mnogo, ali delalcev malo; prosite torej gospodarja žetve, naj pošlje delalcev na žetev svojo.
Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
3 Pojdite; glej, jaz vas pošiljam kakor jagnjeta sredi volkov.
Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
4 Ne nosite mošnje, ne torbe, ne obutala; in nikogar na poti ne pozdravljajte.
Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
5 V kterokoli pa hišo vnidete, naprej recite: Mir tej hiši!
“Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
6 In če bo tu sin mirú, ostal bo mir vaš na njem; če pa ne vrnil se bo k vam.
In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
7 A v tej hiši prebivajte, in jejte in pijte, kar imajo; kajti vreden je delalec plačila svojega. Ne prehajajte iz hiše v hišo.
Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
8 In v kterokoli mesto pridete, in vas sprejmó, jejte, kar vam postavijo,
“Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
9 In uzdravljajte bolnike, kteri so v njej, in pravite jim: Približalo se je k vam kraljestvo Božje.
Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
10 A v kterokoli mesto pridete, in vas ne sprejmó, izidite na ulice njegove in recite:
Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
11 Tudi prah, ki se nas je v mestu vašem prijel, otresamo vam; ali vedite to, da se je približalo k vam kraljestvo Božje.
‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
12 Pravim vam pa, da bo Sodomljanom tisti dan laže, nego temu mestu.
Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
13 Gorjé ti, Korazin! gorjé ti, Betsajda! kajti ko bi se bili v Tiru in Sidonu zgodili čudeži, kteri so se zgodili v vama, bila bi se davno, v žaklji in pepelu sedeč, spokorila.
“‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
14 Ali Tiru in Sidonu bo laže na sodbi, nego vama.
A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
15 In ti, Kapernaum, ki si se do neba povzdignil, zagnan boš do pekla. (Hadēs )
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
16 Kdor posluša vas, posluša mene; in kdor se odreka vas, odreka se mene: a kdor se mene odreka, odreka se tega, kdor me je poslal.
“Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
17 Vrnejo pa se sedemdeseteri z radostjo, govoreč: Gospod, tudi hudiči so nam pokorni v imenu tvojem.
Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
18 Pa jim reče: Videl sem satana, da je padel z neba kakor blisk.
Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
19 Glej, dajem vam oblast stopati na kače in škorpijone, in vso silo vražjo: in nič vam ne bo škodovalo.
Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
20 Ali temu se ne radujte, da so vam hudiči pokorni; radujte se pa marveč, da so imena vaša zapisana na nebesih.
Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
21 V ta čas se oveselí Jezus v duhu, in reče: Zahvaljujem ti, oče, Gospodar neba in zemlje! da si to prikril modrim in razumnim, in si je razodel nedoraslim; dà, oče: ker tako je bila volja tvoja.
A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
22 Vse mi je izročil oče moj; in nikdor ne vé, kdo je sin, razen oče, in kdo je oče, razen sin, in komurkoli če sin razodeti.
“Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
23 In obrnivši se k učencem posebej, reče: Blagor očém, ktere vidijo, kar vi vidite,
Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
24 Kajti pravim vam, da je veliko prerokov in kraljev želelo videti, kar vi vidite, in niso videli; in slišati, kar vi slišite, in niso slišali.
Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
25 In glej, učenik postave vstane, in izkušajoč ga, reče: Učenik, kaj naj storim, da zadobóm večno življenje? (aiōnios )
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
26 On mu pa reče: V zakonu kaj je pisano? kako bereš?
Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
27 On pa odgovarjajoč, reče: "Ljubi Gospoda Boga svojega iz vsega srca svojega, in iz vse duše svoje, in iz vse močí svoje, in iz vse pameti svoje;" in: "a bližnjega svojega kakor samega sebe."
Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
28 Pa mu reče: Prav si odgovoril; to delaj, in živel boš.
Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
29 On pa, hoteč samega sebe opravičiti, reče Jezusu: Kdo pa je bližnji moj?
Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
30 Odgovarjajoč pa Jezus, reče: En človek je šel iz Jeruzalema v Jeriho in je med razbojnike padel, kteri so, ko so ga bili slekli in ranili, odšli, pustivši ga na pol mrtvega.
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
31 Po naključbi pa je šel neki duhoven po tej poti, in videvši ga prejde mimo.
Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
32 Enako pa tudi Levit, ko je bil na tem mestu, pride, in videvši ga, prejde mimo.
Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
33 Neki Samarijan pa, kteri je šel po poti, pride do njega; in ko ga ugleda, zasmili mu se.
Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
34 In pristopivši, obveže mu rane, in vlije olja in vina; in posadivši ga na svoje kljuse, pripelje ga v gostilnico, in poskrbi za-nj.
Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
35 Drugi dan pa, ko je odhajal, vzeme dva srebrnika iz mošnje, in dá krčmarju, in reče mu: Skrbi za-nj; in karkoli več boš potrošil, povrnil ti bom jaz, kedar se vrnem.
Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
36 Kdo torej od teh tréh ti se zdí, da je bil bližnji temu, ki je padel med razbojnike?
“A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
37 On pa reče: Ta, kteri se ga je usmilil. Reče mu torej: Pojdi, tudi ti delaj enako.
Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
38 Zgodí se pa, ko so šli, pa vnide on v eno vas; a neka žena po imenu Marta sprejme ga v hišo svojo.
Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 In ta je imela sestro, ktera se je imenovala Marija, ktera je tudi sedeč pri nogah Jezusovih poslušala besedo njegovo.
Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
40 A Marta si je dajala veliko opraviti s postrežbo; ter pristopi, in reče: Gospod, kaj ti ni mar, da me je sestra moja samo pustila, naj strežem? Reci jej torej, naj mi pomore.
Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
41 Odgovarjajoč pa, reče jej Jezus: Marta! Marta! skrbiš in trudiš se za mnogo;
Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
42 Ali le eno je potrebno. A Marija je dobri del izvolila, kteri jej se ne bo odvzel.
Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”