< Hebrejcem 1 >
1 Potem ko je Bog nekdaj mnogokratno in mnogolično očetom govoril v prerokih,
A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
2 govoril nam je o teh zadnjih dnevih v sinu, Katerega je postavil za dediča vseh stvari, po katerem je tudi svetove naredil, (aiōn )
Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
3 Kateri, odsvit slave in značaj bitja njegovega, in vse noseč z besedo moči svoje, po sebi storivši očiščenje grehov naših, sédel je na desnico veličastva v višavah,
Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
4 In je tolikanj boljši postal od angelov, kolikor odličneje ime je dobil mimo njih.
Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
5 Kajti kateremu je rekel izmed angelov: "Sin moj si ti, jaz sem te danes rodil?" In zopet: "Jaz mu bodem za očeta, in on mi bode za sina?"
Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
6 In ko bode zopet prvorojenca vpeljal v svet, pravi: "In molijo ga naj vsi angeli Božji."
Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
7 In angelom pravi: "On, ki dela angele svoje za vetrove in služabnike svoje za ognja plamen."
A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
8 In sinu: "Prestol tvoj, o Bog, na veka vek. Pravičnosti žezlo je kraljestva tvojega žezlo. (aiōn )
A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn )
9 Ljubil si pravico in sovražil nepostavnost. Zato te je pomazilil Bog, Bog tvoj, z radosti oljem pred tovariši tvojimi."
Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
10 In: "Ti si s konca, Gospod, ustanovil zemljo, in rok tvojih dela so nebesa;
“Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
11 Njih bode konec, ti pa ostaneš; in vsa se bodo postarala kakor obleka,
Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
12 In kakor plašč jih bodeš zvil, in izpremenila se bodo; ti pa si isti, in let tvojih ne bode konec."
Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
13 Kateremu pa izmed angelov je rekel kdaj: "Sédi na desno meni, dokler ne položim sovražnikov tvojih za podnožje nogam tvojim?"
Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
14 Niso li vsi služabni duhovi, v službo pošiljani za nje, ki imajo podedovati zveličanje?
Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?