< Hebrejcem 4 >
1 Bojmo se torej, da se, ko je še ostala obljuba vniti v pokoj njegov, ne vidi, da je kdo izmed vas zaostal.
Saboda haka, sai muyi lura kwarai don kada wani ya kasa kai ga shiga hutun da aka alkawarta maku na Allah.
2 Kajti obljubo smo prejeli, kakor tudi oni; ali onim ni pomagala slišana beseda, ker ni bila pridružena veri njim, ki so slišali.
Don mun ji albishir game da hutun Allah kamar yadda aka fada masu. Amma wancan sakon bai anfana ga wadanda suka ji ba tare da sun bada gaskiya ga sakon ba.
3 Kajti v pokoj vnidemo kateri smo verovali, kakor je rekel: "Da sem prisegel v jezi svoji: Ne vnidejo v pokoj moj," dasì so dela zvršena bila od ustanove svetá.
Ai mu, wadanda muka gaskata-mune zamu shiga wannan hutun, kamar yadda ya ce, “Yadda na yi rantsuwa cikin fushina, baza su shiga hutu na ba.” Ya fadi hakan, ko da yake ya gama aikin hallittarsa tun daga farkon duniya.
4 Kajti rekel je nekje o sedmem dnevi tako: "In počival je Bog sedmi dan od vseh dél svojih."
Domin yayi fadi a wani wuri game da rana ta bakwai, “Allah ya huta a rana ta bakwai daga dukkan ayyukansa.”
5 In v tem zopet: "Ne vnidejo v pokoj moj."
Ya sake cewa, “Baza su taba shiga hutu na ba.”
6 Ker je torej še pričakovati, da vnidejo nekateri vanj, in oni, kateri so prej obljubo prejeli, niso prišli noter zaradi nepokorščine,
Saboda haka, tun da hutun Allah na kebe domin masu su shiga, kuma tun da Isra'ilawa da yawa wadanda suka ji sakon nan mai kyau game da hutunsa ba su shiga ba saboda rashin biyayya,
7 Stavi zopet, neki dan: "Danes" v Davidu govoreč, čez toliko časa, kakor jo rečeno: "Danes, ko začujete glas njegov, ne odrevenite src svojih."
Allah ya sake shirya wata rana da ake kira, “Yau.” Ya sa wannan rana sa'adda yayi magana ta wurin Dauda, wanda ya ce tun da dadewa da aka fara fada, “Yau idan kun ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku.”
8 Kajti ako bi jih bil Jezus upokojil, ne bi potem govoril o drugem dnevi;
Don idan Joshua ya ba su hutu, da Allah ba zai sake magana a kan wata rana ba.
9 Torej čaka sobotni počitek ljudstva Božjega.
Saboda haka, akwai hutun asabar kebabbe ga mutanen Allah.
10 Kajti on, ki je prišel v pokoj njegov, počiva tudi sam od svojih dél, kakor od lastnih Bog.
Don shi wanda ya shiga hutun Allah shi kansa ma ya huta daga ayyukansa, kamar yadda Allah yayi da nasa.
11 Glejmo torej, da vnidemo v ón pokoj, da ne pade kdo v enakem zgledu nepokorščine.
Saboda haka muyi marmarin shiga wancan hutun, don kada kowa ya fadi ga irin rashin biyayyar da suka yi.
12 Živa je namreč beseda Božja, in krepka in ostrejša nego vsak dvorezen meč in pridere noter do ločitve duše in duha, členovja in mozga, in je sodnik naklepov in misli srčnih;
Maganar Allah kuwa rayayyiyace, kuma mai ci, fiye da takobi mai kaifi-biyu. Takan ratsa har tsakanin rai da ruhu, kuma tana kaiwa bargo. Takan iya bincika tunanin zuciya da manufarta.
13 In stvari ni skrite pred njim; vse pa je golo in razodeto očem njega, s katerim imamo opravek.
Babu halittaccen abu da ke boye a idon Allah. Sai dai, kome a sarari yake, kuma a bayyane yake a idonsa wanda lallai ne zamu bada lissafin kanmu a gare shi.
14 Ker imamo torej višjega duhovnika velikega, ki je prehodil nebesa, Jezusa sina Božjega, držímo se spoznanja.
Da yake muna da babban firist wanda ya ratsa sammai, Yesu Dan Allah, sai mu riki bangaskiyarmu da karfi.
15 Kajti nimamo višjega duhovnika, kateri bi ne mogel z nami trpeti slabosti naših, nego izkušanega v vsem enako razen greha.
Domin babban firist namu ba marar tausayi ga kasawarmu bane, amma wanda aka jarraba ne ta ko wanne hali irin yadda aka yi mana, sai dai ba'a same shi da zunubi ba.
16 Bližajmo se torej zaupno prestolu milosti, da zadobimo usmiljenje in najdemo milost za pravočasno pomoč.
Sai mu zo wurin kursiyin alheri gabagadi, domin a yi mana jinkai mu kuwa sami alherin da zai taimake mu a lokacin bukata.