< Apostolska dela 7 >

1 Tedaj reče véliki duhoven: Je li to tako?
Sai babban firist ya ce, ''Wadannan al'amura gaskiya ne?''
2 On pa reče: Možjé bratje in očetje, poslušajte! Bog slave se je prikazal očetu našemu Abrahamu, ko je bil v Mezopotamiji, predno se je nastanil v Haranu,
Sai Istifanus ya amsa ya ce, ''Ya 'yan'uwa da ubanni, ku saurare ni, Allah Madaukaki ya bayyana ga ubanmu Ibrahim tun yana can kasar Mesofotamiya, kafin ma ya zauna a kasar Haran;
3 In rekel mu je: "Izidi iz zemlje svoje, in od rodovine svoje, in pojdi v zemljo, ktero ti bom pokazal."
ya ce masa, 'Ka bar kasarka da danginka, ka tafi kasar da zan nuna maka.'
4 Tedaj je izšel iz zemlje Kaldejske, in nastanil se je v Haranu. In odtod, ko je bil oče njegov umrl, preselil ga je v zemljo, v kterej vi sedaj prebivate.
Sa'annan ya bar kasar Kaldiyawa ya zo ya zauna a Haran; daga can, bayan rasuwar mahaifinsa, sai Allah ya kira shi zuwa wannan kasa da kuke ciki.
5 In ni mu dal nasledstva v njej, ne za stopinjo noge; in obljubil jo je bil njemu dati v posest, in semenu njegovemu za njim, ko še ni imel sina.
Amma Allah bai ba shi kasar gado ba tukuna, ko da misalin tafin sawunsa. Amma ya alkawarta - ko da yake bai riga ya haifi da ba tukuna - wanda zai ba shi kasar gado, shi da zuriyarsa, a bayansa.
6 Rekel pa je Bog tako: "Seme tvoje bo tuje v tujej zemlji, in podvrgli ga bodo sužnosti, in hudo bodo delali ž njim, štiri sto let.
Allah ya yi magana da shi kamar haka, cewa zuriyarsa za su yi bakonci a wata kasa wadda ba tasu ba, mutanen wannan kasar kuwa za su gwada masu bakar azaba su kuma bautar da su har shekaru dari hudu.
7 In narod, kteremu bodo služili, sodil bom jaz," rekel je Bog; "in po tem bodo izšli, in služili bodo meni na tem mestu."
'Kuma zan hukunta wannan al'umma da ta bautar da su,' Allah ya ce, 'Bayan haka za su fito daga wannan kasa su bauta mini a wannan wuri.'
8 In dal mu je zavezo obreze; in tako je rodil Izaka, in obrezal ga je osmi dan; in Izak Jakoba, in Jakob dvanajstere očake.
Allah ya ba Ibrahim alkawarin kaciya, sai Ibrahim ya haifi Ishaku ya yi masa kaciya a rana ta takwas; Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi ubanni Isra'ila su goma sha biyu.
9 In očaki so iz nevošljivosti Jožefa prodali v Egipet; in bil je Bog ž njim.
Wadannan 'yan'uwa suka yi kyashin danuwansu Yusifu suka sayar da shi bauta zuwa Masar. Amma Allah na tare da shi.
10 In rešil ga je iz vseh nadlog njegovih, in dal mu je milost in modrost pred Faraonom kraljem Egiptovskim, in postavil ga je za poglavarja nad Egiptom in vso hišo svojo.
Ya kuwa cece shi daga dukan sharin da yan uwansa suka kulla masa, Allah kuwa ya ba shi tagomashi da hikima a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Fir'auna kuwa ya mai da shi mai mulki a dukan kasar Masar da kuma dukan mallakarsa.
11 Prišla pa je lakota na vso zemljo Egiptovsko in Kanaansko, in velika nadloga; in niso našli živeža očaki naši.
Sai aka yi babbar yunwa a dukan kasar Masar da ta Kan'ana, iyayenmu suka sha wuya saboda rashin abinci.
12 Slišavši pa Jakob, da je žita v Egiptu, poslal je prvikrat očake naše.
Amma lokacin da Yakubu ya ji akwai hatsi a kasar Masar, sai ya aiki ubannimu a karo na farko.
13 In v drugo so spoznali Jožefa bratje njegovi, in znana je postala Faraonu rodovina Jožefova.
Da suka je a karo na biyu, sai Yusifu ya bayyana kansa ga yanuwansa; a wannan lokaci ne Fir'auna ya gane da yanuwan Yusufu.
14 Poslavši pa Jožef, poklical je očeta svojega Jakoba, in vso rodovino svojo, pet in sedemdeset duš.
Yusufu ya aiki yanuwansa su kawo Yakubu ubansu da dukan mallakarsu da iyalansu zuwa Masar, Dukansu mutane saba'in da biyar ne.
15 In sešel je Jakob v Egipet, in umrl je on in očetje naši;
Yakubu ya tafi ya zauna a Masar; shi da zuriyarsa har mutuwar su.
16 In prenesli so jih v Sihem, in položili v grob, kterega je kupil Abraham za ceno srebra od sinov Hemorja očeta Sihemovega.
Aka dauke su zuwa Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya da kudin azurfa daga hannun yayan Hamor a Shekem.
17 Ko se je pa bližal čas obljube, ktero je prisegel Bog Abrahamu, narastlo je ljudstvo in umnožilo se v Egiptu,
Yayin da alkawarin Allah ya kusato wanda Allah ya fada wa Ibrahim, mutanen suka karu suka hayayyafa kwarai a Masar,
18 Dokler ni vstal drugi kralj, kteri ni poznal Jožefa.
Sai a ka yi wani sarki a Masar wanda bai san Yusifu ba,
19 Ta je zvijaško storil z rodom našim, in zatrl je očete naše, da so morali izpostavljati otroke svoje, da ne živé.
Wannan sarki ya yaudari kakkaninmu ya yi masu mugunta kwarai da gaske, har ma ya kai ga suna barin jariransu cikin hasari don su ceci rayukansu.
20 V ta čas se je rodil Mojzes, in bil je prijeten Bogu: kteri je bil tri mesece rejen v hiši očeta svojega.
A wannan lokaci ne aka haifi Musa, kuma kyakkyawan yaro ne sai aka yi renon sa tsawon wata uku a gidan mahaifinsa a asirce.
21 A ko je izpostavljen bil, vzela ga je hči Faraonova, in odgojila ga je sebi za sina.
Yayin da aka jefar da shi, sai diyar Fir'auna ta dauke shi ta rene shi kamar danta.
22 In naučil se je Mojzes vse modrosti Egiptovske; in bil je mogočen v besedah in v dejanjih.
Aka ilimantar da Musa da dukan ilimi irin na Masar; kuma ya shahara cikin fasahar magana da kuma ayyukansa.
23 Ko je pa dopolnil štirideset let, prišlo mu je na misel obiskati brate svoje sinove Izraelove.
Amma lokacin da yakai shekara arba'in, sai ya yi niyyar ya ziyarci 'yan'uwansa, Isra'ilawa.
24 In ko je videl nekoga, da trpí krivico, obranil ga je, in maščeval je tega, kteri je krivico trpel, in ubil je Egipčana.
Sai ya ga wani na cin zalin Ba Isra'ile, Musa kuwa ya taimaki wanda ake kwara ta wurin murkushe Bamasaren:
25 Menil je pa, da bratje njegovi umejo, da jim po njegovej roki hoče dati Bog odrešenje ali oni niso razumeli.
zaton Musa 'yan'uwansa za su fahimci taimakon Allah ne ya zo masu amma ina! Basu gane ba.
26 A drugi dan je prišel k njim, ko so se bojevali, in miril jih je, govoreč: "Možjé, vi ste bratje; po kaj delate krivico eden drugemu?"
Washegari ya ga wasu Isra'ilawa na fada da junansu; ya yi kokari ya raba su; sai ya ce masu, 'Malamai, ku 'yan'uwan juna ne; don me kuke fada da junanku?'
27 Tisti pa, ki je delal krivico bližnjemu, odpahne ga, govoreč: Kdo te je postavil za poglavarja in sodnika nad nami?
Amma shi wanda ake kwarar makwabcinsa ya ture Musa a gefe guda, ya ce, 'Wa ya nada ka shugaba ko alkali akanmu?
28 Ali me ti hočeš ubiti, kakor si ubil včeraj Egipčana?"
Kana so ka kashe ni ne, kamar yadda ka kashe Bamasaren nan jiya?'
29 Mojzes je pa pobegnil na to besedo, in bil je tujec v zemlji Madijamskej, kjer je rodil dva sina.
Da jin haka sai Musa ya gudu, zuwa kasar Midinawa, a matsayin dan gudun hijira. Anan ya haifi ''ya'ya biyu maza.
30 In ko se je dopolnilo štirideset let, prikazal mu se je v puščavi gore Sinajske angelj Gospodov v plamenu gorečega grma.
Bayan da shekaru arba'in suka wuce, sai mala'ika ya bayyana gare shi a jeji, kusa da dutsen Sinai, a cikin harshen wuta a cikin jeji.
31 Mojzes pa, ko je to videl, začudil se je prikazni; in ko je pristopil, da bi pogledal, oglasil mu se je glas Gospodov:
Sa'adda Musa ya ga wutar, mamaki ya kama shi; sai ya maso kusa don ya kara dubawa, sai ya ji muryar Ubangiji na cewa,
32 " Jaz sem Bog očetov tvojih, Bog Abrahamov in Bog Izakov in Bog Jakobov." Mojzes pa je strepetal, in ni upal pogledati.
'Nine Allah na ubanninka, Ibrahim, da na Ishaku, da na Yakubu.' Musa ya razana har ma bai sake daga kai ya duba ba.
33 Reče pa mu Gospod: "Izuj obutalo z nog svojih; kajti mesto, na kterem stojiš, sveta je zemlja.
Ubangiji ya ce masa, 'Tube takalminka, domin in da kake tsaye wuri mai tsarki ne.
34 Dobro sem videl stisko naroda svojega, ki je v Egiptu, in njih zdihovanje sem slišal; in sešel sem, da jih rešim. In sedaj pridi, poslal te bom v Egipet."
Ba shakka na ga wahalar da mutane na ke sha a Masar, kuma na ji nishinsu, don haka na zo in cece su, yanzu fa sai ka zo, in aike ka zuwa Masar.'
35 Tega Mojzesa, kteremu so se bili uprli, govoreč: "Kdo te je postavil za poglavarja in sodnika? tega je Bog za poglavarja in odrešenika poslal po roki angelja, kteri mu se je bil prikazal v grmu.
Wannan fa shine Musan da suka ki, harma da cewa, 'Wanene ya nada ka alkali ko shugaba a kanmu?' Shine kuma wanda Allah ya aiko masu a matsayin shugaba da kuma mai ceto. Allah ya aiko shi ta hannun mala'ikan da ya gani a daji.
36 Ta jih je izpeljal, delajoč čudeže in znamenja v zemlji Egiptovskej in Rdečem morji, in v puščavi štirideset let.
Bayan alamu da al'ajibai iri-iri a Masar da kuma Baharmaliya, Musa ya fito da su daga Masar da kuma cikin jeji, a lokacin da suka yi tafiya shekara arbain.
37 Ta je tisti Mojzes, ki je rekel sinovom Izraelovim: "Preroka vam bo obudil Gospod Bog izmed bratov vaših, kakor mene; njega poslušajte."
Wannan shine Musan da ya cewa Isra'ilawa, 'Ubangiji zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin Yan'uwan ku.'
38 Ta je tisti, ki je bil pri množici v puščavi z angeljem, kteri mu je govoril na gori Sinajskej, in z očeti našimi, kteri je prejel besede življenja, da jih nam dá;
Wannan shine mutumin da ke tare da mutane a jeji. Karkashin jagorancin mala'ikan da ya yi magana da shi a dutsen Sinai. Wannan ne mutumin da ke tare da ubannen mu, wannan shi ne mutumin da ya ba mu maganar Allah mai rai.
39 Kteremu niso hoteli pokorni biti očetje naši, nego so ga zavrgli, in obrnili srca svoja v Egipet,
Wannan shine mutumin da ubannenmu suka ki su yi masa biyayya; su ka fitar da shi daga cikinsu, suka kudurta a zuciyarsu za su koma masar.
40 Rekši Aronu: "Naredi nam bogove, kteri bodo hodili pred nami; kajti ta Mojzes, ki nas je izpeljal iz zemlje Egiptovske, ne vémo, kaj mu se je zgodilo."
A lokacin ne suka cewa Haruna, 'ya yi masu allolin da za su jagorance su zuwa masar. Domin kuwa ga zancen Musan nan da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'
41 In vlili so tele tiste dni, in darovali so daritev maliku, in veselili so se del rok svojih.
Sai suka kera dan maraki suka kawo wa gunkin hadaya, suka yi murna da abin da hannayensu suka kera.
42 In odvrnil se je Bog, in izdal jih je, naj služijo ozvezdju neba, kakor je pisano v bukvah prerokov: "Ali ste mi darovali zaklanice in daritve štirideset let v puščavi, hiša Izraelova?
Allah ya bashe su su bauta wa tauraran sama, kamar yadda yake a rubuce cikin littattafafan annabawa, 'Kun mika mani hadayu na yankakkun dabbobi a jeji ne a shekaru arba'in din nan ya ku Isra'ilawa?'
43 In ponesli ste šator Molohov, in zvezdo boga svojega Remfana, podobe, ktere ste naredili, da ste jim se poklanjali; in preselil vas bom za Babilon."
Kun yarda da haikalin Molek da kuma tauraron allahn nan Rafem, da kuma siffofin nan da kuka kera don ku yi masu sujada; don haka zan kai ku bauta har gaba da Babila.'
44 Šator pričevanja so imeli očetje naši v puščavi, kakor jim je zapovedal ta, ki je rekel Mojzesu, naj ga naredí po podobi, ktero je videl;
Kakkaninmu suna da alfarwa ta sujada domin shaida a cikin jeji, kamar yadda Allah ya umarta yayin da ya yi magana da Musa, cewa ya yi shi bisa ga salon da aka nuna mashi.
45 Kterega so tudi prejeli očetje naši, in ponesli z Jezusom, v posestvo poganov, ktere je izgnal Bog izpred obličja očetov naših, noter do dnî Davida;
Wannan shine Alfarwar da kakkaninmu suka zo da shi, a lokacin Joshuwa. Wannan ya faru ne yayin da suka mallaki wannan kasa ta al'ummai da Allah ya kora a gaban kakkaninmu. Haka abin yake har ya zuwa zamanin Dauda,
46 Kteri je milost našel pred Bogom, in je prosil, da bi našel prebivališče Bogu Jakobovemu.
wanda ya sami tagomashi a wurin Allah; don ya gina masujada domin Allah na Yakubu.
47 A Solomon mu je sezidal hišo.
Amma Sulaimanu ne ya gina Gidan Allah.
48 Ali Najviši ne prebiva v tempeljnih z rokami narejenih, kakor prerok pravi:
Sai dai Madaukaki ba yakan zauna a gidan da hannaye suka gina ba, kamar yadda annabin ya ce,
49 "Nebo mi je stol, in zemlja podnožje nogam mojim. Kakošno hišo mi boste zidali? pravi Gospod. Ali ktero je mesto za počivanje moje?
'Sama kursiyina ce, duniya kuwa wurin ajjiye sawayena ne. To wane irin gida za ku gina mani? inji Ubangiji: ko kuwa ina ne wurin da zan huta?
50 Ni li roka moja vsega tega naredila?"
Ko ba hannayena ne suka yi dukan wadannan ba?'
51 Trdovratni in neobrezanih src in ušes! vi se vedno Duhu svetemu upirate; kakor očetje vaši, tudi vi.
Ku mutane masu taurin kai masu zuciya mara kaciya da kunnuwa marasa ji, kullum kuna gaba da Ruhu Mai Tsarki, kuna aikata abin da kakkaninku suka aikata.
52 Kterega od prerokov niso pregnali očetje vaši? In pomorili so te, kteri so naprej oznanili prihod pravičnega, kakor izdajalci in ubijalci ste sedaj vi postali;
Wane annabi ne kakkaninku ba su tsanantawa ba? Sun kashe annabawan da suka rigayi zuwan Mai Adalcin nan, kuma kun zama wadanda suka kasance masu bashe shi da masu kashe shi,
53 Kteri ste prejeli postavo po naredbi angeljev, in je niste ohranili.
kune mutanen da kuka karbi shari'a wadda mala'iku suka bayar, amma ba ku kiyaye ta ba”.
54 Ko so pa to slišali, togotili so se v srcih svojih, in škripali so z zobmí zoper njega.
Yayin da majalisar suka ji wannan, sai ransu ya baci kwarai, har suna cizon hakoransu don gaba da Istifanus.
55 On pa, poln Duha svetega, ozrè se na nebo, in ugleda slavo Božjo, in Jezusa, da stojí na desnici Božjej.
Amma shi, cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya daga idonsa sama, ya ga daukakar Allah; ya kuma hango Yesu na tsaye a hannun daman Allah.
56 In reče: Glej, vidim nebesa odprta, in sina človečjega, da stoji na desnici Božjej.
Istifanus ya ce, “Duba, ina ganin sama ta bude, ga Dan Mutum na tsaye a hannun dama na Allah.”
57 In zakričavši z močnim glasom, zataknejo ušesa svoja, in planejo ene misli na-nj.
Amma yan majalisar suka daga murya da karfi, suka yi ihu, suka kuma toshe kunnuwansu, gaba dayansu suka afka masa;
58 In izpahnivši ga ven iz mesta, pobijali so ga s kamenjem. In priče so položile oblačila svoja pred noge mladeniču, kteremu je bilo imel Savel.
suka fitar da shi bayan gari, suka jejjefe shi da duwatsu, don shaida sai suka tube manyan rigunansu suka ajiye a gaban wani matashi da ake ce da shi Shawulu.
59 In pobijali so s kamenjem Štefana, kteri je klical in govoril: Gospod Jezus, sprejmi duh moj!
Lokacin da suke kan jifan Istifanus, ya dinga kira yana cewa, ''Ya Ubangiji Yesu, ka karbi ruhu na.”
60 In pokleknivši, zavpije z močnim glasom: Gospod, ne postavi jim tega greha! In rekši to, zaspal je.
Ya durkusa ya daga murya da karfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka rike wannan zunubi a kansu.” Yayin da ya fadi wannan, sai ya yi barci.

< Apostolska dela 7 >