< Apostolska dela 3 >
1 A Peter in Janez sta šla vkupej gor v tempelj ob uri molitve, ob devetih.
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 In nosili so nekega moža, kteri je hrom bil iz telesa matere svoje; in pokladali so ga vsak dan pred tempeljnova vrata, ktera se imenujejo Lepa, da je prosil miloščine od teh, kteri so hodili v tempelj.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 Ta, videvši Petra in Janeza, da hočeta iti v tempelj, prosil je, da bi prejel miloščine.
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 Peter pa, pogledavši na-nj z Janezom, reče: Poglej na naju!
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 In on je gledal na nju, misleč, da bo kaj prejel od nju.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 Peter pa reče: Srebra in zlata nimam; kar pa imam, to ti dam. V ime Jezusa Kristusa Nazarečana, vstani in hodi!
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 In prijemši ga za desno roko, vzdigne ga: in precej so se utrdila stopala njegova in gležnji.
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 In poskočivši, stal je in hodil, in vnide ž njima v tempelj, hodeč in poskakujoč in hvaleč Boga.
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 In videlo ga je vse ljudstvo da hodi in hvali Boga;
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 In poznali so ga, da je tisti, ki je za voljo miloščine sedel pri Lepih vratih tempeljnovih in napolnijo se strmenja in groze nad tem, kar mu se je prigodilo.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 Ko se je pa hromi ta, ki je bil ozdravel, držal Petra in Janeza, priteče k njim vse ljudstvo v lopo, ki se imenuje Solomonova, in strmeli so.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 Videč pa to Peter, odgovorí ljudstvu: Možjé Izraelci! kaj se čudite temu, ali kaj naju gledate, kakor da bi bila s svojo močjó ali oblastjo storila, da ta hodi?
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 Bog Abrahamov, in Izakov, in Jakobov, Bog očetov naših oslavil je sina svojega Jezusa, kterega ste vi izdali, in zatajili ga pred obličjem Pilatovim, ko je on sodil, naj se izpustí.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 A vi ste svetnika in pravičnega zatajili, in prosili ste, naj vam dá ubijalca.
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 A začetnika življenja ste umorili, kterega je Bog obudil iz mrtvih, čemur smo mi priče.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 In za voljo vere v ime njegovo je tega, ki ga vidite in poznate, utrdilo ime njegovo; in vera, ki je po njem, dala mu je popolno to zdravje vpričo vseh vas.
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 Ali sedaj, bratje, vém, da ste iz nevednosti storili, kakor tudi poglavarji vaši.
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 Bog pa, kar je bil naprej oznanil z ustmi vseh prerokov svojih, da bo Kristus trpel, dopolnil je tako.
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 Spokorite se torej in izpreobrnite, da se izbrišejo grehi vaši: da pridejo časi ohlajenja od obličja Gospodovega,
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 In pošlje oznanjenega vam Jezusa Kristusa,
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 Kterega mora sicer nebo sprejeti do časov, ko se uravna vse, kar je Bog povedal z ustmi svetih prerokov svojih od nekedaj. (aiōn )
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn )
22 Mojzes namreč je rekel očakom: "Preroka vam bo zbudil Gospod Bog vaš izmed bratov vaših, kakor mene; njega poslušajte v vsem, karkoli vam bo govoril.
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 Bo pa, da vsaka duša, ktera ne bo poslušala tega preroka, iztrebila se bo iz ljudstva."
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 Pa tudi vsi preroki od Samuela in po tem, kolikorkoli jih je govorilo, oznanili so te dní.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 Vi ste sinovi prerokov in zaveze, ktero je storil Bog z očaki našimi, govoreč Abrahamu: "In v semenu tvojem se bodo blagoslovili vsi narodi zemlje."
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 Vam najprej je zbudil Bog sina svojega Jezusa, in poslal, da vas blagoslovi, da se vsak od vas obrne od hudobij svojih.
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”