< Apostolska dela 13 >
1 Bili so pa v cerkvi, ktera je bila v Antijohiji, nekteri preroki in učeniki: Barnaba in Simeon, ki se je imenoval Niger, in Lucij Cirenec, in Manahen, s Herodom četrtnikom odgojen, in Savel.
A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu.
2 Ko so pa oni službo Gospodu opravljali in se postili, reče sveti Duh: Odločite mi Barnaba in Savla za delo, na ktero sem ju poklizal.
Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su”.
3 Tedaj, postivši se in molivši, položé roke na nju, ter ju odpusté.
Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.
4 Ta torej, poslana od Duha svetega, snideta v Selevcijo, in odtod se odpeljeta po morji na Ciper.
Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus.
5 In ko sta prišla v Salamino, oznanjevala sta besedo Božjo po shajališčih Judovskih; imela sta pa tudi Janeza za služabnika.
Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.
6 In ko sta prešla otok noter do Pafa, najdeta nekega vražarja, lažnjivega preroka Juda, kteremu je bilo ime Barjezu,
Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya.
7 In je bil z namestnikom Sergijem Pavlom, pametnim možem. Ta, poklicavši Barnaba in Savla, želel je slišati besedo Božjo.
Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah.
8 Ali ustavljal jima se je Elima, vražar (tako namreč se tolmači ime njegovo), gledajoč, da bi namestnika odvrnil od vere.
Amma Elimas “mai tsafi” (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.
9 Savel pa, ki se tudi Pavel imenuje, poln Duha svetega, pogledavši na-nj,
Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido.
10 Reče: O polni vsake zvijače in vsake hudobije, sin hudičev, sovražnik vsake pravice! ali ne boš nehal prevračati pravih potov Gospodovih?
Sai ya ce, “Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?
11 In sedaj, glej, roka Gospodova je zoper té, in slep boš in ne boš videl solnca do časa. In pri tej priči je padel na-nj mrak in tema, in tipajoč okoli, iskal je vodnika.
Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci.” Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora.
12 Tedaj je namestnik, ko je videl, kaj se je zgodilo, veroval, in čudil se je nauku Gospodovemu.
Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.
13 Odpeljavši pa se iz Pafa Pavel in kteri so bili ž njim, pridejo v Pergo Pamfilijsko. Janez pa se loči od nju, in vrne se v Jeruzalem.
Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima.
14 Ona pa, ko sta bila odšla iz Perge, prideta v Antijohijo Pisidijsko, in vnideta v sobotni dan v shajališče, in sedeta.
Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna.
15 Po branji postave in prerokov pa pošljejo poglavarji shajališča k njima, govoreč: Moža brata! če je v vaju beseda tolažbe za ljudstvo, govorita.
Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, “'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi.”
16 Vstavši torej Pavel, pomigne z roko, naj umolknejo, ter reče: Možjé Izraelci, in kteri se bojite Boga, poslušajte!
Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, “Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji.
17 Bog naroda tega Izraelovega je izvolil očete naše, in povišal je ljudstvo, ko so prebivali v zemlji Egiptovskej, in s povzdigneno roko jih je izpeljal iž nje.
Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta.
18 In okoli štirideset let je potrpel ž njih šegami v puščavi.
Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.
19 In pokončavši sedem narodov v zemlji Kanaanskej, razdelil jim je po kocki njih zemljo.
Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado.
20 In po tem, kakih štiri sto in petdeset let, dal jim je sodnike do Samuela preroka.
Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.
21 In odtlej so zahtevali kralja, in dal jim je Bog Savla sina Kisovega, moža iz rodú Benjaminovega, štirideset let.
Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in.
22 In ko je bil tega zavrgel, obudil jim je Davida za kralja, kteremu je tudi rekel, pričevaje: "Našel sem Davida Jesejevega, moža po srcu svojem, kteri bo izpolnjeval vso voljo mojo."
Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.
23 Iž njegovega semena je Bog po obljubi obudil Izraelu zveličarja Jezusa,
Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi.
24 Ko je oznanil Janez pred prihodom njegovim krst pokore vsemu ljudstvu Izraelovemu.
Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila.
25 Ko je pa Janez tek svoj dopolnjeval, govoril je: "Kdo menite, da sem jaz? Nisem jaz, nego glej, prišel bo za menoj, komur nisem vreden obutala odvezati z nog."
Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'
26 Možjé bratje, sinovi rodú Abrahamovega, in kteri se med vami bojé Boga! vam se je poslala beseda tega življenja.
Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto.
27 Kajti tí, kteri prebivajo v Jeruzalemu, in njih poglavarji, ker tega niso poznali, odsodili so ga, in tako so glasove prerokov, kteri se vsako soboto beró, dopolnili;
Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.
28 In nobene krivice smrtne niso našli, in prosili so Pilata, naj ga pogubí.
Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi.
29 In ko so dopolnili vse, kar je bilo pisano za njega, sneli so ga z lesa in položili v grob.
Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
30 A Bog ga je obudil iz mrtvih,
Amma Allah ya tashe shi daga matattu.
31 In pokazoval se je več dnî tem, kteri so bili ž njim vred prišli iz Galileje v Jeruzalem, kteri so priče njegove pred ljudstvom.
Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
32 In mi vam oznanjujemo obljubo, ktera se je obljubila očetom, da je to Bog izpolnil nam njih otrokom, obudivši Jezusa,
Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu.
33 Kakor je tudi v drugem psalmu pisano: "Sin moj si ti; jaz sem te danes rodil."
Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: ''Kai da na ne yau na zama mahaifinka.''
34 Da ga je pa obudil iz mrtvih, da se ne vrne več v trohnenje, rekel je tako: "Dal vam bom svetinjo Davidovo zvesto."
Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: ''Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu.''
35 Za to pravi tudi na drugem mestu: "Ne boš dal, da bi svetnik tvoj videl trohnenje."
Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.'
36 Kajti David, ko je bil ob času svojem poslužil volji Božjej, zaspal je, in položili so ga k očetom njegovim, in videl je trohnenje.
Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba,
37 Ta pa, ki ga je Bog obudil, ni videl trohnenja.
amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
38 Znano vam torej bodi, možjé bratje! da vam se po njem odpuščanje grehov oznanjuje;
'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
39 In od vsega, od česar se v Mojzesovej postavi niste mogli opravičiti, opravičil se bo v tem vsak, kdor veruje.
Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
40 Glejte torej, da ne pride na vas, kar je rečeno v prerokih:
Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku:
41 "Glejte, zaničevalci! in čudite se in izginite; kajti delo bom jaz storil v dnéh vaših, delo, kteremu ne boste verovali, če vam kdo pové."
'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku.”
42 Ko sta pa izšla iz shajališča Judovskega, prosili so ju pogani, naj bi jim drugo soboto govorila te besede.
Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa.
43 In ko se je zbor razšel, odšlo je veliko Judov in pobožnih izpreobrnencev za Pavlom in Barnabom, ktera sta, govoreč jim, prigovarjala, naj ostanejo v milosti Božjej.
Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
44 A drugo soboto se je skoro vse mesto zbralo, da bi slišali besedo Božjo.
Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji.
45 Videč pa Judje ljudstvo, napolnijo se nenavidnosti, in govorili so zoper to, kar je pravil Pavel, nasprotujoč in preklinjajoč.
Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.
46 Tedaj Pavel in Barnaba srčno rečeta: Vam se je morala najprej govoriti beseda Božja; ko jo pa zametujete, in se nevredne štejete večnega življenja, glej, obračava se do poganov. (aiōnios )
Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, “Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. (aiōnios )
47 Kajti tako nam je zapovedal Gospod: "Postavil sem te za luč poganom, da boš na zveličanje noter do kraja zemlje."
Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'”
48 Ko so pa pogani to slišali, veselili so se, in slavili so besedo Gospodovo, in verovali so, kolikor jih je bilo odločenih za večno življenje. (aiōnios )
Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. (aiōnios )
49 In razširjala se je beseda Gospodova po vsej deželi.
Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.
50 Judje pa nadražijo pobožne in poštene žene in prvake mestne, in zbudé preganjanje zoper Pavla in Barnaba, in izženó ju iz svojih krajev.
Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu.
51 A ona sta otresla prah z nog svojih na njih, in prišla sta v Ikonijo.
Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya.
52 Učenci pa so so napolnjevali radosti in Duha svetega.
Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.