< Apostolska dela 12 >

1 V ta čas pa vzdigne Herod kralj roke, da bi nektere od cerkve mučil.
A lokacin nan Sarki Hiridus ya sa wa wasu masu bi hannu domin ya musguna masu.
2 In umorí Jakoba brata Janezovega z mečem.
Ya kashe Yakubu dan'uwan Yahaya da takobi.
3 In videvši, da je po godi Judom, sklene tudi Petra vjeti (bili so pa dnevi presnih kruhov);
Bayan da ya ga hakan ya gamshi Yahudawa, sai ya kama Bitrus ma.
4 Kterega je tudi vjel in posadil v ječo, in izročil štirim četvericam vojakov, naj ga varujejo, in hotel ga je po Velikej noči izpeljati pred ljudstvo.
Bayan ya kama shi, sai ya tsare shi a kurkuku ya kuwa sa sojoji hudu su dinga tsaron sa; yana niyyar kawo shi gaban mutanen a bayan Idin katarewa.
5 Petra torej so sicer varovali v ječi; a cerkev je molila za-nj k Bogu neprenehoma.
To, Bitrus na tsare a kurkuku, amma 'yan'uwa na iklisiya suna yin addu'a ga Allah sosai domin sa.
6 Ko ga je pa imel Herod izpeljati, tisto noč je spal Peter med dvema vojakoma, okovan v dvojne verige; a varuhi pred vratmi so stražili ječo.
Ana kamar gobe Hiridus zai fitar da shi, a wannan daren, Bitrus yana barci a tsakanin sojoji biyu, daure da sarkoki biyu; sojoji kuma na gadi a bakin kurkukun.
7 In glej, angelj Gospodov pristopi, in svetloba se zasveti v ječi; in udarivši Petra v rebra, zbudí ga, govoreč: Vstani hitro! In spadle so mu verige z rok.
Ba zato, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gareshi, haske ya haskaka dakin. Ya taba Bitrus a gefe ya tashe shi kuma ya ce, “Tashi da sauri.” Sai ga sarkokin suka zube daga hannunsa.
8 In reče mu angelj: Opaši se, in obuj opanke svoje. In storil je tako. In reče mu: Ogrni plašč svoj, in pojdi za menoj.
Mala'ikan ya ce masa, “Yi damara ka sa takalmanka.” Bitrus kuwa yayi haka. Mala'ikan ce ma sa, “Yafa mayafinka, ka biyo ni.”
9 In izšel je, in šel je za njim; in ni vedel, da je res, kar se je godilo po angelji, nego menil je, da vidi prikazen.
Bitrus kuwa ya bi mala'ikan suka fita waje. Bai gane abin da mala'ikan ke yi zahiri ne ba. Yana zaton ko yana ganin wahayi ne.
10 Ko sta bila pa prešla mimo prve straže in druge, prideta do železnih vrat, ktera so držala v mesto, in ta jima se sama od sebe odpró. Ter izideta, in prideta v eno ulico, in precej odstopi angelj od njega.
Bayan da suka wuce masu tsaron fari da na biyu, sun kai kofar da aka yi da karfe wadda ta mike zuwa cikin gari; ta bude masu da kanta. Suka fita sun bi titin, kuma nan take kuma sai mala'ikan ya bar shi.
11 In ko pride Peter k sebi, reče: Sedaj vém res, da je poslal Gospod angelja svojega, in me je otel iz roke Herodove in vsega čakanja ljudstva Judovskega.
Da Bitrus ya komo hayyacin sa, ya ce, “Hakika yanzu na gane Ubangiji ya aiko da mala'ikansa don ya kubutar da ni daga hannun Hiridus da abin da Yahudawa suke zato.”
12 In razmislivši to, pride do hiše Marije matere Janeza s priimkom Marka, kjer je bilo veliko zbranih, kteri so molili.
Da ya gane haka, ya zo gidan Maryamu mahaifiyar Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus; masu bi da yawa sun taru a can suna addu'a.
13 Ko je pa Peter na vežna vrata potrkal, pristopi deklica po imenu Roda poslušat.
Da ya kwankwasa kofar gidan, sai baiwar gidan mai suna Roda ta zo don ta bude kofar.
14 In spoznavši glas Petrov, od veselja ni odprla vrat, nego odbežala je noter, in sporočila je, da stojí Peter pred vratmi.
Da ta gane muryar Bitrus, don farin ciki ta kasa bude kofar; maimakon haka, ta koma daki a guje, don ta basu labari Bitrus na tsaye a bakin kofa.
15 Oni jej pa rekó: Meša ti se. A ona je trdila, da je tako. Oni so pa govorili: Angelj njegov je.
Suka ce mata, “Kin haukace.” Amma ta nace da cewa haka ne. Suka ce, “Mala'ikansa ne.”
16 A Peter je čakal in trkal. Ko pa odpró, ugledajo ga, in ostrmé.
Amma Bitrus ya ci gaba da kwankwasawa, da suka bude kofar, sai suka ga ai shine, suka sha mamaki kwarai.
17 Namignivši pa z roko, naj molčé, razloží jim, kako ga je Gospod izpeljal iz ječe. In reče: Sporočite to Jakobu in bratom. In izšel je, in odšel je v drugi kraj.
Bitrus kuwa ya yi masu hannu yana, masu alama su yi shuru. Sai ya gaya masu labarin yadda Ubangiji ya kubutar da shi daga kurkukun. Ya ce, “Ku gaya wa Yakubu da dukan 'yan'uwa abin da ya faru.” Sai ya bar su, ya tafi wani wuri.
18 Ko se je pa zdanilo, ni bil majhen strah med vojaki, kaj da se je s Petrom zgodilo.
Sa'anda gari ya waye ba karamar hargowa ce ta tashi a cikin sojojin ba, game da abin da ya faru da Bitrus.
19 Herod pa, ko ga je zahteval in ga ni našel, izpraša varuhe, in ukaže jih odpeljati: in snide iz Judeje v Cezarejo, ter je tu živel.
Bayan da Hiridus ya neme shi kuma bai same shi ba, sai ya tambayi masu tsaron kuma ya bada umarni a kashe su. Sai ya gangara daga Yahudiya zuwa Kaisariya ya yi zamansa a can.
20 Bil je pa Herod jezen na Tirce in Sidonce; a oni enodušno pridejo k njemu, in pregovorivši Blasta komornika kraljevega, prosili so mirú, za to, ker je njih dežela dobivala živež iz kraljeve.
Yanzu kuwa Hiridus ya yi fushi sosai da mutanen Taya da Sidon. Suka tafi wurinsa tare. Suka roki Bilastasa, mataimakin sarkin, ya taimake su. Sai suka nemi sasantawa don suna samun abinci daga kasarsa ne.
21 A odločeni dan se je oblekel Herod v kraljevo oblačilo, in sedši na sodišče, govoril jim je.
A ranan da aka kayyade, Hirudus ya sha damara da kayan saurata kuma ya zauna akan kursiyi; ya yi masu jawabi.
22 Ljudstvo pa je vpilo: Božji glas je to, a ne človeški.
Mutanen suka yi ihu, “Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!”
23 Pri tej priči pa ga je udaril angelj Gospodov, za to ker ni dal slave Bogu: in sneden od črvov je umrl.
Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.
24 A beseda Gospodova je rastla in razširjala se.
Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya.
25 A Barnaba in Savel sta se vrnila iz Jeruzalema, ko sta bila opravila službo, in vzela sta s seboj tudi Janeza s priimkom Marka.
Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne. [Barnaba da Shawulu suka koma Urushalima.]

< Apostolska dela 12 >