< Razodetje 21 >

1 In videl sem novo nebo in novo zemljo, kajti prvo nebo in prva zemlja sta prešla in ni bilo več morja.
Sai na ga sabuwar sama da sabuwar duniya, domin sama ta fari da duniya ta fari sun shude, ba kuma teku.
2 In jaz, Janez, sem videl sveto mesto, novi Jeruzalem, prihajati dol od Boga, iz nebes, pripravljeno, kakor je nevesta okrašena za svojega soproga.
Na ga birni mai tsarki, sabuwar Urushalima, wadda ta sauko kasa daga sama wurin Allah, shiryayya kamar amaryar da aka yi wa ado domin mijinta.
3 In zaslišal sem močan glas z neba, rekoč: »Glej, šotorsko svetišče Boga je z ljudmi in prebival bo z njimi in oni bodo njegovi ljudje in sam Bog bo z njimi in bo njihov Bog.
Na ji babbar murya daga kursiyinta na cewa, “Duba! Mazaunin Allah yana tare da 'yan adam, zai zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kuma da kansa zai kasance tare da su ya kuma zama Allahnsu.
4 In Bog bo obrisal vse solze z njihovih oči; in ne bo več smrti, niti bridkosti, niti jokanja, niti ne bo več nobene bolečine, kajti prejšnje stvari so minile.«
Zai share dukan hawaye daga idanunsu, kuma babu sauran mutuwa, ko bakinciki, ko kuka, ko azaba. Abubuwan da sun shude.
5 In tisti, ki je sedel na prestolu, je rekel: »Poglej, vse stvari delam nove.« In rekel mi je: »Zapiši, kajti te besede so resnične in zveste.«
Shi wanda yake zaune a kan kursiyin ya ce, “Duba! Na maida kome ya zama sabo.” Ya ce, “Ka rubuta wannan domin wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya”.
6 In rekel mi je: »Končano je. Jaz sem Alfa in Omega, začetek in konec. Temu, ki je žejen, bom zastonj dal iz studenca vode življenja.
Ya ce mani, “Wadannan abubuwan an gama! Ni ne Alpha da Omega, farko da karshe. Ga mai jin kishi, zan bashi kyauta daga mabulbular ruwan rai.
7 Kdor premaga, bo podedoval vse stvari; in jaz bom njegov Bog, on pa bo moj sin.
Wanda ya ci nasara, zai gaji wadannan abubuwa, ni kuma zan zama Allahnsa, shi kuma ya zama da na.
8 Toda strahopetci, neverniki, gnusneži, morilci, vlačugarji, čarodeji, malikovalci in vsi lažnivci bodo imeli svoj delež v jezeru, ki gori z ognjem in žveplom, kar je druga smrt.« (Limnē Pyr g3041 g4442)
Amma ga matsorata, da marasa bangaskiya, da masu kazanta, da masu kisan kai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da dukan makaryata, mazaunin su zai kasance cikin tafki mai ci da farar wuta. Mutuwa ta biyu kenan.” (Limnē Pyr g3041 g4442)
9 In k meni je prišel eden izmed sedmih angelov, ki so imeli sedem stekleničk, polnih sedmih zadnjih nadlog in govoril z menoj, rekoč: »Pridi sèm, pokazal ti bom nevesto, Jagnjetovo ženo.«
Daya daga cikin mala'ikun bakwai ya zo wurina, wanda yake dauke da tasoshi bakwai cike da annobai bakwai na karshe, yace, “Zo nan. Zan nuna maka amarya, matar Dan Rago”.
10 In v duhu me je odvedel proč, k veliki in visoki gori in mi pokazal tisto veliko mesto, sveti Jeruzalem, ki se je od Boga spuščal z neba,
Sai ya dauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsawo ya nuna mani birni mai-tsarki, Urushalima, tana saukowa daga cikin sama daga wurin Allah.
11 ki je imel Božjo slavo in njegova svetloba je bila podobna najdragocenejšemu kamnu, celó podobna kamnu jaspisu, čistemu kakor kristal;
Urushalima tana da daukakar Allah, shekinta yana kama da dutse mai tamani, sai kace dutsen yasfa, garau kamar karau.
12 in imelo je veliko in visoko obzidje in dvanajst velikih vrat in ob velikih vratih dvanajst angelov in na njih so bila napisana imena, ki so imena dvanajsterih rodov Izraelovih otrok:
Tana da babban garu mai tsawo, da kofofi goma sha biyu, da mala'iku goma sha biyu a kofofin. Akan kofofin an rubuta sunayen kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila.
13 na vzhodu troje velikih vrat, na severu troje velikih vrat, na jugu troje velikih vrat in na zahodu troje velikih vrat.
A gabas akwai kofofi uku, a arewa kofofi uku, a kudu kofofi uku, da kuma yamma kofofi uku.
14 In obzidje mesta je imelo dvanajst temeljev in na njih imena dvanajsterih Jagnjetovih apostolov.
Garun birnin yana da harsashin gini goma sha biyu, a bisansu akwai sunaye goma sha biyu na manzanni goma sha biyu na Dan Rago.
15 In tisti, ki je govoril z menoj, je imel zlat trst, da izmeri mesto in njegova velika vrata in njegovo obzidje.
Shi wanda yayi magana dani yana da sandan awo na zinariya domin ya auna birnin, da kofofinsa, da garunsa.
16 In mesto leži štirioglato in dolžina je tako velika kakor širina; in s trstom je izmeril mesto, dvanajst tisoč dolžin brazd. Njegova dolžina in širina in višina so enake.
Birnin; da tsawonsa da fadinsa iri daya ne. Ya gwada birnin da sandar awo, mil dubu sha biyu a tsaye (fadinsa, da tsawonsa, da tsayinsa duka daya ne)
17 In izmeril je njegovo obzidje: sto štiriinštirideset komolcev, glede na človeško mero, to je, od angela.
Ya kuma gwada garunsa, kamu 144, bisa ga gwajin 'yan adam (wanda shine ma'aunin mala'ika).
18 In obzidje je bilo zgrajeno iz jaspisa in mesto je bilo čisto zlato, podobno čistemu steklu.
An gina garun da Yasfa birnin kuma da sahihiyar zinariya, mai kama da madubi mai kyalli.
19 In temelji mestnega obzidja so bili okrašeni z vsemi vrstami dragocenih kamnov. Prvi temelj je bil jaspis, drugi safir, tretji kalcedon, četrti smaragd,
An kawata harsashin garun da kowanne irin dutse mai tamani. Na fari yasfa, na biyu saffir, na uku agat, na hudu emerald,
20 peti sardoniks, šesti sardij, sedmi hrizolit, osmi beril, deveti topaz, deseti hrizopraz, enajsti hijacint, dvanajsti ametist.
na biyar Onis, na shida sardiyus, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha daya yakinta, na sha biyu kuma ametis.
21 In dvanajst velikih vrat je bilo dvanajst biserov; vsaka posamezna velika vrata so bila iz enega bisera in ulica mesta je bila čisto zlato, kakor bi bilo prosojno steklo.
Kofofi goma sha biyu lu'u-lu'ai ne goma sha biyu; kowacce daya a cikin kofofin daga lu'u-lu'u daya aka yi shi. Titunan birnin kuwa zinariya ce sahihiya, sai kace madubi garau.
22 In v njem nisem videl templja, kajti njegov tempelj sta Gospod Bog Vsemogočni in Jagnje.
Ban ga haikali a cikin birnin ba, gama Ubangiji Allah Mai iko duka da Dan Ragon su ne haikalinsa.
23 In mesto ni potrebovalo sonca niti lune, da bi sijala nanj, kajti razsvetljevala ga je Božja slava in Jagnje je njegova svetloba.
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi gama daukakar Allah ta haskaka shi, kuma fitilarsa Dan Rago ne.
24 In narodi teh, ki so rešeni, bodo hodili v njegovi svetlobi in kralji zemlje vanj prinesejo svojo slavo in čast.
Al'ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin. Sarakunan duniya kuma za su kawo daukakarsu cikinsa.
25 In njegova velika vrata se podnevi sploh ne bodo zaprla, kajti tam ne bo noči.
Kofofinsu kuma ba za a rufe su da rana ba, babu dare kuma a can.
26 In vanj bodo prinesli slavo in čast narodov.
Za su kawo daukaka da darajar al'ummai a cikinsa,
27 In tja nikakor ne bo stopilo karkoli, kar omadežuje niti karkoli počne ogabno ali počne laž, temveč tisti, ki so zapisani v Jagnjetovi knjigi življenja.
babu wani abu mai kazanta da zai taba shiga cikinsa. Ko wanda yake aikata abin kunya da karya, sai wadanda an rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Dan Rago kadai.

< Razodetje 21 >