< Psalmi 88 >
1 Oh Gospod Bog, rešitev moje duše, pred teboj sem klical dan in noč.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Naj moja molitev pride predte, svoje uho nagni k mojemu klicu,
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 kajti moja duša je polna stisk in moje življenje se bliža grobu. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 Prištet sem s tistimi, ki gredo dol v jamo. Sem kakor človek, ki nima moči.
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Svoboden med mrtvimi, kakor umorjeni, ki ležijo v grobu, ki se jih ne spominjaš več in so iztrebljeni iz tvoje roke.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Položil si me v najglobljo jamo, v temo, v globine.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Tvoj bes trdno leži na meni in prizadel si me z vsemi svojimi valovi. (Sela)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Mojega znanca si postavil daleč od mene, njim si me naredil [za] ogabnost; zaprt sem in ne morem priti ven.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Moje oko žaluje zaradi stiske; Gospod, vsak dan sem klical k tebi, svoje roke sem iztegoval k tebi.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Hočeš mrtvim pokazati čudeže? Mar bodo mrtvi vstali in te hvalili? (Sela)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Bo tvoja ljubeča skrbnost oznanjena v grobu? Ali tvoja zvestoba v propadu?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Bodo tvoji čudeži spoznani v temi? In tvoja pravičnost v deželi pozabljivosti?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Toda jaz sem klical k tebi, oh Gospod in zjutraj te bo moja molitev prestregla.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Gospod, zakaj zavračaš mojo dušo? Zakaj skrivaš svoj obraz pred menoj?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Prizadet sem in od svoje mladosti pripravljen umreti; medtem ko trpim tvoje strahote, sem raztresen.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Tvoj kruti bes gre prek mene, tvoje strahote so me uničile.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Vsak dan so prišli okoli mene kakor voda, skupaj so me obkrožali.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Ljubega in prijatelja si postavil daleč od mene in mojega znanca v temo.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.