< Psalmi 17 >

1 Usliši iskrenega, oh Gospod, bodi pozoren na moj klic, pazljivo prisluhni moji molitvi, ki ne prihaja iz hlinjenih ustnic.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Naj moja razsodba pride iz tvoje prisotnosti, naj tvoje oči gledajo stvari, ki so pravične.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Preizkusil si moje srce, obiskal si me ponoči, preizkusil si me, pa ničesar nisi našel; odločen sem, da moja usta ne bodo grešila.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Kar se tiče človeških del, sem se po besedi tvojih ustnic varoval pred stezami uničevalca.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Podpiraj mojo smer življenja po tvojih stezah, da moje stopinje ne zdrsnejo.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 Klical sem k tebi, kajti uslišal me boš, oh Bog. Nagni k meni svoje uho in usliši moj govor.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Pokaži svojo čudovito ljubečo skrbnost, oh ti, ki s svojo desnico rešuješ tiste, ki svoje trdno upanje polagajo vate pred tistimi, ki se vzdigujejo proti njim.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Varuj me kakor zenico očesa, skrij me pod senco svojih peruti,
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 pred zlobnimi, ki me zatirajo, pred mojimi smrtnimi sovražniki, ki me obdajajo naokrog.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 Zajeti so v svojo lastno maščobo. S svojimi usti govorijo ponosno.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 Sedaj so nas obdali na naših korakih. Svoje oči so naravnali in pripognili k zemlji,
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 kakor lev, ki je pohlepen po svojem plenu in kakor bi bil mlad lev, ki preži na skrivnih krajih.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Vzdigni se, oh Gospod, razočaraj ga, vrzi ga dol. Osvobodi mojo dušo pred zlobnim, kar je tvoj meč,
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 pred ljudmi, ki so tvoja roka, oh Gospod, pred ljudmi sveta, ki imajo svoj delež v tem življenju in katerih trebuh napolnjuješ s svojim skritim zakladom. Polni so otrok in preostanek svojega imetja zapustijo svojim otročičem.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Kar se mene tiče, bom v pravičnosti gledal tvoj obraz. Ko se zbudim, bom nasičen s tvojo podobnostjo.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalmi 17 >