< Psalmi 102 >

1 Usliši mojo molitev, oh Gospod in moje vpitje naj pride do tebe.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Svojega obraza ne skrivaj pred menoj na dan, ko sem v stiski; nagni k meni svoje uho. Na dan, ko kličem, mi naglo odgovori.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Kajti moji dnevi so použiti kakor dim in moje kosti so sežgane kakor ognjišče.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Moje srce je prizadeto in ovenelo kakor trava, tako da pozabljam jesti svoj kruh.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Zaradi glasu mojega stokanja se moje kosti lepijo na mojo kožo.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Podoben sem pelikanu iz divjine; podoben sem sovi v puščavi.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Bedim in sem kakor vrabec sam na strehi.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Moji sovražniki me ves dan grajajo in tisti, ki so besni name, prisegajo zoper mene.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Kajti pepel sem jedel kakor kruh in svojo pijačo sem mešal z jokom,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 zaradi tvojega ogorčenja in tvojega besa, kajti vzdignil si me in me vrgel dol.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Moji dnevi so kakor senca, ki se zmanjšuje in izsušen sem kakor trava.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Toda ti, oh Gospod, boš ostal na veke in tvoj spomin vsem rodovom.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Vstal boš in imel usmiljenje do Siona, kajti čas, da mu [izkažeš] naklonjenost, da, določeni čas je prišel.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Kajti tvoji služabniki uživajo v njegovih kamnih in so naklonjeni njegovemu prahu.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Tako se bodo pogani bali Gospodovega imena in vsi kralji zemlje tvoje slave.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Ko bo Gospod zgradil Sion, se bo prikazal v svoji slavi.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Upošteval bo molitev revežev in ne bo preziral njihove molitve.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 To bo zapisano za prihajajoči rod; in ljudstvo, ki bo ustvarjeno, bo hvalilo Gospoda.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Kajti on je pogledal dol iz višine svojega svetišča, z nebes je Gospod pogledal zemljo,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 da usliši stokanje jetnika, da osvobodi tiste, ki so določeni za smrt,
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 da oznani Gospodovo ime na Sionu in njegovo hvalo v Jeruzalemu,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 ko se zberejo skupaj ljudstva in kraljestva, da služijo Gospodu.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Oslabil je mojo moč na poti, skrajšal je moje dneve.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Rekel sem: »Oh moj Bog, ne odstrani me v sredi mojih dni; tvoja leta so skozi vse rodove.«
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Od davnine si položil temelj zemlji in nebo je delo tvojih rok.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ta [dva] bosta izginila, toda ti boš ostal. Da, vsa se bosta postarala kakor obleka; zamenjal ju boš kakor suknjo in bosta zamenjani,
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 toda ti si isti in tvoja leta ne bodo imela konca.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Otroci tvojih služabnikov bodo nadaljevali in njihovo seme bo utrjeno pred teboj.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalmi 102 >