< 4 Mojzes 27 >
1 Potem so prišle hčere Celofháda, sinú Heferja, sinú Gileáda, sinú Mahírja, sinú Manáseja, od družin Jožefovega sina Manáseja, in to so imena hčera: Mahla, Noa, Hogla, Milka in Tirca.
’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
2 Obstale so pred Mojzesom, pred duhovnikom Eleazarjem, pred princi in vso skupnostjo, pri vratih šotorskega svetišča skupnosti, rekoč:
Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
3 »Naš oče je umrl v divjini in ni bil v skupini tistih, ki so se zbrali skupaj zoper Gospoda, v Korahovi skupini, temveč je umrl v svojem lastnem grehu in ni imel sinov.
“Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
4 Zakaj bi bilo ime našega očeta odpravljeno od njegove družine, ker ni imel sina? Dajte nam torej posest med brati našega očeta.«
Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
5 Mojzes je njihovo zadevo privedel pred Gospoda.
Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
6 Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
7 »Celofhádove hčere govorijo pravilno. Zagotovo jim boš dal posest dediščine med brati njihovih očetov in povzročil jim boš, da bo dediščina njihovega očeta prešla k njim.
“Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
8 Izraelovim otrokom boš govoril, rekoč: ›Če mož umre in nima sina, potem boste njegovi dediščini povzročili, da preide na njegovo hčer.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
9 Če pa nima hčere, potem boste njegovo dediščino dali njegovim bratom.
In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
10 In če nima bratov, potem boste njegovo dediščino dali bratom njegovega očeta.
In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
11 In če njegov oče nima bratov, potem boste njegovo dediščino dali njegovemu sorodniku, ki je poleg njega, iz njegove družine in ta jo bo vzel v last in to bo Izraelovim otrokom zakon razsodbe, ‹« kakor je Gospod zapovedal Mojzesu.
In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
12 Gospod je rekel Mojzesu: »Povzpni se gor na to goro Abarím in poglej deželo, ki sem jo dal Izraelovim otrokom.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
13 Ko jo boš videl, boš tudi ti zbran k svojemu ljudstvu, kakor je bil zbran tvoj brat Aron.
Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
14 Kajti uprla ste se zoper mojo zapoved v Cinski puščavi, v prepiru skupnosti, da me izkažeta svetega pri vodi, pred njihovimi očmi, to je vodi iz Meríbe v Kadešu, v Cinski divjini.«
gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
15 Mojzes je spregovoril Gospodu, rekoč:
Musa ya ce wa Ubangiji,
16 »Naj Gospod, Bog duhov vsega mesa, postavi moža nad skupnost,
“Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
17 ki bo lahko odhajal pred njimi in ki bo lahko prihajal pred njimi in ki jih bo lahko vodil ven in ki jih bo lahko privedel noter, da Gospodova skupnost ne bo kakor ovce, ki nimajo pastirja.«
yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
18 Gospod je rekel Mojzesu: »Vzemi si Nunovega sina Józueta, moža, v katerem je duh in svojo roko položi nanj
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
19 in ga postavi pred duhovnika Eleazarja in pred vso skupnost in mu daj zadolžitev v njihovih očeh.
Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
20 Nekaj od svoje časti boš položil nanj, da bo vsa skupnost Izraelovih otrok lahko poslušna.
Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
21 Ta bo stal pred duhovnikom Eleazarjem, ki bo pred Gospodom zanj iskal nasvet po razsodbi urima. Na njegovo besedo bodo odhajali ven in na njegovo besedo bodo prihajali noter, tako on kot vsi Izraelovi otroci z njim, celo vsa skupnost.«
Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
22 Mojzes je storil kakor mu je Gospod zapovedal. Vzel je Józueta in ga postavil pred duhovnika Eleazarja in pred vso skupnost
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
23 in svoji roki položil nanj in mu dal zadolžitev, kakor je Gospod zapovedal po Mojzesovi roki.
Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.