< Marko 7 >
1 Potem so prišli skupaj k njemu farizeji in nekateri izmed pisarjev, ki so prišli iz Jeruzalema.
Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.
2 In ko so videli nekatere izmed njegovih učencev jesti kruh z omadeževanimi, to se pravi z neumitimi rokami, so našli krivdo.
Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba,
3 Kajti farizeji in vsi Judje ne jedo, razen če si svojih rok pogosto ne umivajo, ker se držijo izročila starešin.
(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa.
4 In ko pridejo iz trga, ne jedo, razen če se ne umijejo. In mnogo drugih stvari je, ki so jih sprejeli, da se jih drže, kot umivanje čaš in vrčev, bakrenih posod in miz.
Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
5 Potem so ga farizeji in pisarji vprašali: »Zakaj tvoji učenci ne živijo glede na izročilo starešin, temveč jedo kruh z neumitimi rokami?«
Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, “Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?”
6 Odgovoril je in jim rekel: »Dobro je Izaija prerokoval o vas hinavcih, kakor je pisano: ›Ti ljudje me spoštujejo s svojimi ustnicami, toda njihovo srce je daleč od mene.‹
Amma ya amsa masu cewa, “Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni.
7 Čeprav me zaman obožujejo, ker za nauke učijo človeške zapovedi.
Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'”.
8 Ker se z odlaganjem Božje zapovedi na stran držite človeških izročil, kakor je umivanje čaš in vrčev in počnete še mnoge druge takšne stvari.«
Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane.
9 In rekel jim je: »Prav dobro zavračate Božjo zapoved, da bi lahko obdržali svoje lastno izročilo.
Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane.
10 Kajti Mojzes je rekel: ›Spoštuj svojega očeta in svojo mater, ‹ in: ›Kdorkoli preklinja očeta ali mater, naj življenje konča s smrtjo, ‹
Koda shike Musa ya rubuta cewa, “ka girmama Ubanka da Uwarka”, kuma, “duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take”.
11 toda vi pravite: ›Če bo človek rekel svojemu očetu ali materi: ›To je korbán, to se pravi dar, po čemerkoli bi lahko imel korist od mene, ‹ bo prost.‹
Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, “duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)”'.
12 In mu nič več ne dovolite, da bi za svojega očeta ali svojo mater karkoli storil.
Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu.
13 S svojim izročilom, ki ste ga izročili, delate Božjo besedo brez učinka in počnete mnogo takšnih podobnih stvari.«
Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi.”
14 In ko je k sebi poklical vso množico, jim je rekel: »Vsak izmed vas naj mi prisluhne in razume:
Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, “ku kasa kunne gareni, kuma ku gane.
15 ›Nič ni zunaj človeka, kar bi ga z vstopanjem vanj lahko omadeževalo, toda besede, ki pridejo iz njega, te so tiste, ki omadežujejo človeka.‹
Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi”
16 Če ima katerikoli človek ušesa, da slišijo, naj posluša.«
Bari mai kunnen ji, ya ji.
17 Ko je od množice vstopil v hišo, so ga njegovi učenci vprašali glede prispodobe.
Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali.
18 In reče jim: »Ali ste tudi vi tako brez razumevanja? Ali ne zaznate, da ga katerakoli stvar, ki od zunaj vstopa v človeka, ta ne more omadeževati,
Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba,
19 ker ta ne vstopa v njegovo srce, temveč v trebuh in gre ven v zunanje stranišče, očiščujoč vso hrano?«
domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga”. Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
20 In rekel je: »To, kar prihaja iz človeka, to omadežuje človeka.
Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi
21 Kajti od znotraj, iz človekovega srca, izvirajo zle misli, zakonolomstva, prešuštva, umori,
Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa,
22 tatvine, pohlepnost, zlobnost, prevara, pohotnost, hudoben pogled, bogokletje, ponos, nespametnost;
zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci.
23 vse te zle stvari prihajajo od znotraj in omadežujejo človeka.«
Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi.”
24 In vstal je od tam ter odšel v meje Tira in Sidóna in vstopil v hišo in hotel, da tega ne bi izvedel noben človek, toda ni mogel ostati skrit.
Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba.
25 Kajti neka ženska, katere mlada hči je imela nečistega duha, je slišala o njem in prišla ter padla k njegovim stopalom.
Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa.
26 Ženska je bila Grkinja, Sirofeničanka po rodu, in rotila ga je, da bi iz njene hčere izgnal hudiča.
Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
27 Toda Jezus ji je rekel: »Naj bodo najprej nasičeni otroci, kajti ni primerno vzeti kruha otrokom in ga vreči psom.«
Sai ya ce mata, “Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba”.
28 Ona pa je odgovorila in mu rekla: »Da, Gospod, vendar psi pod mizo jedo od otroških drobtin.«
Sai ta amsa masa cewa, “I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan.”
29 In rekel ji je: »Zaradi tega govora pojdi svojo pot; hudič je izšel iz tvoje hčere.«
Ya ce mata, “domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki.”
30 In ko je prišla k svoji hiši, je spoznala, da je hudič izšel in svojo hčer [našla] ležečo na postelji.
Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
31 In spet, ko je odšel iz tirskih in sidónskih pokrajin, je prišel h Galilejskemu morju, skozi sredo krajev Deseteromestja.
Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis.
32 In k njemu prinesejo nekoga, ki je bil gluh in je imel motnjo v svojem govoru in rotili so ga, naj nanj položi svojo roko.
Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
33 In vzel ga je proč od množice in svoja prsta položil v njegova ušesa in pljunil ter se dotaknil njegovega jezika
Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa.
34 in zroč k nebu, je vzdihnil ter mu rekel: »Efatá!« to je: »Odpri se.«
Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, “Ifatha”, wato, “bude!”
35 In njegova ušesa so se nemudoma odprla in vez njegovega jezika se je sprostila in je jasno govoril.
Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
36 In naročil jim je, da naj ne povedo nobenemu človeku, toda bolj, kot jim je naročal, toliko bolj na veliko so to razglašali,
Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina.
37 in bili so preko mere osupli, rekoč: »Vse stvari je storil dobro; tako gluhim daje slišati, kakor nemim govoriti.«
kuma suna ta mamaki cewa, “Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana.”