< Marko 7 >

1 Potem so prišli skupaj k njemu farizeji in nekateri izmed pisarjev, ki so prišli iz Jeruzalema.
Farisiyawa da waɗansu malaman dokoki waɗanda suka zo daga Urushalima, suka taru kewaye da Yesu.
2 In ko so videli nekatere izmed njegovih učencev jesti kruh z omadeževanimi, to se pravi z neumitimi rokami, so našli krivdo.
Sai suka ga waɗansu daga cikin almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta, wato, da ba a wanke ba.
3 Kajti farizeji in vsi Judje ne jedo, razen če si svojih rok pogosto ne umivajo, ker se držijo izročila starešin.
(Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci, sai sun wanke hannuwa sarai tukuna, yadda al’adun dattawa suka ce.
4 In ko pridejo iz trga, ne jedo, razen če se ne umijejo. In mnogo drugih stvari je, ki so jih sprejeli, da se jih drže, kot umivanje čaš in vrčev, bakrenih posod in miz.
Sa’ad da suka dawo daga wurin kasuwanci, dole su wanke hannu kafin su ci abinci. Sukan kuma kiyaye waɗansu al’adu da yawa, kamar wanken kwafuna, tuluna da butoci.)
5 Potem so ga farizeji in pisarji vprašali: »Zakaj tvoji učenci ne živijo glede na izročilo starešin, temveč jedo kruh z neumitimi rokami?«
Saboda haka, Farisiyawa da malaman dokoki suka tambayi Yesu, suka ce, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun dattawa, a maimakon haka suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta?”
6 Odgovoril je in jim rekel: »Dobro je Izaija prerokoval o vas hinavcih, kakor je pisano: ›Ti ljudje me spoštujejo s svojimi ustnicami, toda njihovo srce je daleč od mene.‹
Ya amsa ya ce, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci game da ku munafukai; kamar yadda yake a rubuce cewa, “‘Waɗannan mutane da baki suke girmama ni, amma zukatansu sun yi nesa da ni.
7 Čeprav me zaman obožujejo, ker za nauke učijo človeške zapovedi.
A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokokin mutane ne kawai.’
8 Ker se z odlaganjem Božje zapovedi na stran držite človeških izročil, kakor je umivanje čaš in vrčev in počnete še mnoge druge takšne stvari.«
Kun yar da umarnan Allah, kuna bin al’adun mutane.”
9 In rekel jim je: »Prav dobro zavračate Božjo zapoved, da bi lahko obdržali svoje lastno izročilo.
Ya kuma ce musu, “Kuna da hanya mai sauƙi na ajiye umarnan Allah a gefe ɗaya, don ku kiyaye al’adunku!
10 Kajti Mojzes je rekel: ›Spoštuj svojega očeta in svojo mater, ‹ in: ›Kdorkoli preklinja očeta ali mater, naj življenje konča s smrtjo, ‹
Gama Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’kuma, ‘Duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.’
11 toda vi pravite: ›Če bo človek rekel svojemu očetu ali materi: ›To je korbán, to se pravi dar, po čemerkoli bi lahko imel korist od mene, ‹ bo prost.‹
Amma ku, kukan ce, in mutum ya ce wa mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da ya kamata ku samu daga wurina, Korban ne,’ (wato, abin da aka keɓe wa Allah),
12 In mu nič več ne dovolite, da bi za svojega očeta ali svojo mater karkoli storil.
sa’an nan haka ba kwa ƙara barinsa yă yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa wani abu.
13 S svojim izročilom, ki ste ga izročili, delate Božjo besedo brez učinka in počnete mnogo takšnih podobnih stvari.«
Ta haka kuke rushe maganar Allah ta wurin al’adun da kuke miƙa wa’ya’yanku. Haka kuma kuke yin abubuwa da yawa.”
14 In ko je k sebi poklical vso množico, jim je rekel: »Vsak izmed vas naj mi prisluhne in razume:
Sai Yesu ya sāke kiran taron wurinsa ya ce, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimci wannan.
15 ›Nič ni zunaj človeka, kar bi ga z vstopanjem vanj lahko omadeževalo, toda besede, ki pridejo iz njega, te so tiste, ki omadežujejo človeka.‹
Ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. Sai dai abin da ya fita daga cikin mutum ne, yake ƙazantar da shi.”
16 Če ima katerikoli človek ušesa, da slišijo, naj posluša.«
17 Ko je od množice vstopil v hišo, so ga njegovi učenci vprašali glede prispodobe.
Bayan ya bar taron, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
18 In reče jim: »Ali ste tudi vi tako brez razumevanja? Ali ne zaznate, da ga katerakoli stvar, ki od zunaj vstopa v človeka, ta ne more omadeževati,
Ya ce, “Ashe, ba ku da saurin ganewa? Ba ku gane cewa ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi.
19 ker ta ne vstopa v njegovo srce, temveč v trebuh in gre ven v zunanje stranišče, očiščujoč vso hrano?«
Gama ba ya shiga cikin zuciyarsa, sai dai cikin tumbinsa, sa’an nan kuma yă fita daga jikinsa.” (Da faɗin haka, Yesu ya nuna tsabtar kowane irin abinci.)
20 In rekel je: »To, kar prihaja iz človeka, to omadežuje človeka.
Ya ci gaba, “Abin da yake fitowa daga mutum ne yake ƙazantar da shi.
21 Kajti od znotraj, iz človekovega srca, izvirajo zle misli, zakonolomstva, prešuštva, umori,
Gama daga ciki, daga zuciyar mutane, mugayen tunani suke fitowa, fasikanci, sata, kisankai, zina,
22 tatvine, pohlepnost, zlobnost, prevara, pohotnost, hudoben pogled, bogokletje, ponos, nespametnost;
kwaɗayi, ƙeta, ruɗu, ƙazantaccen sha’awa, kishi, ɓata suna, girman kai da kuma wauta.
23 vse te zle stvari prihajajo od znotraj in omadežujejo človeka.«
Duk waɗannan mugayen abubuwa daga cikin suke fitowa, suna kuma ƙazantar da mutum.”
24 In vstal je od tam ter odšel v meje Tira in Sidóna in vstopil v hišo in hotel, da tega ne bi izvedel noben človek, toda ni mogel ostati skrit.
Sai Yesu ya bar wurin, ya kuma tafi wajajen Taya. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa yă sani ba. Duk da haka, bai iya ɓoye kasancewarsa ba.
25 Kajti neka ženska, katere mlada hči je imela nečistega duha, je slišala o njem in prišla ter padla k njegovim stopalom.
Da jin labarinsa, sai wata mace wadda ƙaramar diyarta tana da mugun ruhu, ta zo ta durƙusa a gabansa.
26 Ženska je bila Grkinja, Sirofeničanka po rodu, in rotila ga je, da bi iz njene hčere izgnal hudiča.
Macen kuwa mutuniyar Hellenawa ce, an haife ta a Funisiya a Suriya. Ta roƙi Yesu yă fitar da aljani da yake jikin diyarta.
27 Toda Jezus ji je rekel: »Naj bodo najprej nasičeni otroci, kajti ni primerno vzeti kruha otrokom in ga vreči psom.«
Yesu ya ce mata, “Da farko, bari’ya’ya su ci su ƙoshi tukuna, gama ba daidai ba ne, a ɗauki burodin yara a jefa wa karnukansu.”
28 Ona pa je odgovorila in mu rekla: »Da, Gospod, vendar psi pod mizo jedo od otroških drobtin.«
Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, ko karnuka ma da suke ƙarƙashin tebur, sukan ci burbuɗin da suke fāɗuwa daga abincin yara.”
29 In rekel ji je: »Zaradi tega govora pojdi svojo pot; hudič je izšel iz tvoje hčere.«
Sai ya ce mata, “Saboda irin wannan amsa, ki tafi, aljanin ya rabu da diyarki.”
30 In ko je prišla k svoji hiši, je spoznala, da je hudič izšel in svojo hčer [našla] ležečo na postelji.
Ta tafi gida, ta tarar da diyarta kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.
31 In spet, ko je odšel iz tirskih in sidónskih pokrajin, je prišel h Galilejskemu morju, skozi sredo krajev Deseteromestja.
Sai Yesu ya bar wajajen Taya, ya bi ta Sidon har zuwa Tekun Galili da kuma cikin yankin Dekafolis.
32 In k njemu prinesejo nekoga, ki je bil gluh in je imel motnjo v svojem govoru in rotili so ga, naj nanj položi svojo roko.
A can ne waɗansu mutane suka kawo masa wani kurma, wanda da ƙyar yake magana. Sai suka roƙe shi yă ɗibiya hannunsa a kan mutumin.
33 In vzel ga je proč od množice in svoja prsta položil v njegova ušesa in pljunil ter se dotaknil njegovega jezika
Bayan da ya jawo shi gefe, sai Yesu ya sa yatsotsinsa a kunnuwan mutumin, ya tofa miyau ya kuma taɓa harshen mutumin.
34 in zroč k nebu, je vzdihnil ter mu rekel: »Efatá!« to je: »Odpri se.«
Ya ɗaga kai sama, ya ja numfashi mai zurfi, sa’an nan ya ce masa, “Effata!” (Wato, “Buɗe!”).
35 In njegova ušesa so se nemudoma odprla in vez njegovega jezika se je sprostila in je jasno govoril.
Bayan ya faɗa haka, sai kunnuwan mutumin suka buɗe, harshensa kuma ya kunce, sai ya fara magana sarai.
36 In naročil jim je, da naj ne povedo nobenemu človeku, toda bolj, kot jim je naročal, toliko bolj na veliko so to razglašali,
Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi.
37 in bili so preko mere osupli, rekoč: »Vse stvari je storil dobro; tako gluhim daje slišati, kakor nemim govoriti.«
Mutane suka cika da mamaki, suka ce, “Kai, ya yi kome daidai. Har ma yana sa kurame su ji, bebaye kuma su yi magana.”

< Marko 7 >