< Luka 22 >

1 Torej približal se je praznik nekvašenega kruha, ki se imenuje Pasha.
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 Visoki duhovniki in pisarji pa so si prizadevali, kako bi ga lahko ubili, kajti bali so se ljudi.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 Tedaj je Satan vstopil v Juda, z vzdevkom Iškarijot, ki je bil izmed dvanajsterih.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 In ta je odšel svojo pot ter se posvetoval z visokimi duhovniki in stotniki, kako bi jim ga lahko izdal.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 In ti so bili veseli in se obvezali, da mu dajo denar.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 In obljubil je ter iskal priložnost, da jim ga izda v odsotnosti množice.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 Potem je prišel dan nekvašenega kruha, ko mora biti zaklano pashalno jagnje.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 In poslal je Petra ter Janeza, rekoč: »Pojdita in nam pripravita pashalno jagnje, da bomo lahko jedli.«
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 In rekla sta mu: »Kje želiš, da ga pripraviva?«
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 Rekel jima je: »Glejta, ko vstopita v mesto, vaju bo srečal moški, nesoč lončen vrč vode; sledita mu v hišo, v katero vstopa.
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 Hišnemu očetu pa bosta rekla: ›Učitelj ti pravi: ›Kje je soba za goste, kjer bom s svojimi učenci jedel pashalno jagnje?‹‹
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 In pokazal vama bo veliko opremljeno zgornjo sobo; tam pripravita.«
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 In onadva sta odšla ter našla, kakor jima je rekel in pripravila sta pashalno jagnje.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 Ko pa je prišla ura, se je usedel in dvanajsteri apostoli z njim.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 Rekel jim je: »S hrepenenjem sem si želel, da bi to pashalno jagnje jedel z vami, še predem trpim,
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 kajti povem vam: ›Ne bom več jedel od tega, dokler to ne bo izpolnjeno v Božjem kraljestvu.‹«
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 In vzel je čašo ter se zahvalil in rekel: »Vzemite jo in si to razdelite med seboj,
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 kajti povem vam: ›Ne bom pil od sadu vinske trte, dokler ne pride Božje kraljestvo.‹«
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 In vzel je kruh in se zahvalil in ga razlomil ter jim dal, rekoč: »To je moje telo, ki je dano za vas, to delajte v spomin name.«
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 Podobno tudi čašo po večerji, rekoč: »Ta čaša je nova zaveza v moji krvi, ki se preliva za vas.
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 Toda glejte, roka tistega, ki me izdaja, je z menoj pri mizi.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 In Sin človekov resnično gre, kakor je bilo določeno, toda gorje temu človeku, po katerem je izdan!«
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 In med seboj so se začeli spraševati, kdo izmed njih je bil, da bi storil to stvar.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 Med njimi pa je bil tudi prepir, kdo izmed njih naj bi veljal za največjega.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 On pa jim je rekel: »Kralji poganov izvajajo gospostvo nad njimi, in kateri izvajajo oblast nad njimi, so imenovani dobrotniki.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 Toda vi ne bodite takšni, temveč kdor je med vami največji, naj bo kakor mlajši in kdor je šef kakor tisti, ki streže.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 Kajti kdo je večji, kdor sedi pri mizi ali kdor streže? Mar ni, kdor sedi pri mizi? Toda jaz sem med vami kakor tisti, ki streže.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 Vi ste tisti, ki ste vztrajali z menoj v mojih skušnjavah.
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 In določam vam kraljestvo, kakor ga je moj Oče določil meni,
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 da boste lahko jedli in pili pri moji mizi v mojem kraljestvu in sedeli na prestolih ter sodili dvanajst Izraelovih rodov.«
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 In Gospod je rekel: »Simon, Simon, glej, Satan je zahlepel, da bi te imel, da te lahko preseje kakor pšenico,
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 toda jaz sem molil zate, da tvoja vera ne opeša; ko pa boš spreobrnjen, okrépi svoje brate.«
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 In ta mu je rekel: »Gospod, pripravljen sem iti s teboj, tako v ječo, kakor v smrt.«
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 On pa je rekel: »Povem ti, Peter, danes petelin ne bo zapel, preden ne boš trikrat zatajil, da me poznaš.«
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 In rekel jim je: »Ko sem vas poslal brez mošnje in malhe in čevljev ali vam je karkoli manjkalo?« In rekli so: »Nič.«
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 Potem jim je rekel: »Toda kdor ima mošnjo, naj jo sedaj vzame in prav tako svojo malho; in kdor nima meča, naj proda svojo obleko in enega kupi.
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 Kajti povem vam, da se mora na meni dovršiti še to, kar je pisano: ›In prištet je bil med prestopnike, ‹ kajti stvari glede mene imajo konec.«
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 In rekli so: »Gospod, glej, tukaj sta dva meča.« On pa jim je rekel: »Dovolj je.«
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 In prišel je ven ter odšel, kakor je bil navajen, na Oljsko goro in tudi njegovi učenci so mu sledili.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 Ko pa je bil na mestu, jim je rekel: »Molíte, da ne vstopite v skušnjavo.«
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 In od njih je bil oddaljen približno za lučaj kamna ter pokleknil in molil,
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 rekoč: »Oče, če si voljan, odstrani to čašo od mene, vendar ne moja volja, temveč tvoja naj se zgodi.«
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 In prikazal se mu je angel iz nebes ter ga krepil.
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 Medtem ko je bil v neznosni bolečini, pa je še iskrenejše molil in njegov pot je bil, kakor bi na zemljo padale velike kaplje krvi.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 In ko se je dvignil od molitve in prišel k svojim učencem, jih je zaradi bridkosti našel speče
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 in jim rekel: »Čemu spite? Vstanite in molíte, da ne vstopite v skušnjavo.«
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 In medtem ko je še govoril, zagleda množico in tisti, ki se je imenoval Juda, eden izmed dvanajsterih, je šel pred njimi in se približal Jezusu, da bi ga poljubil.
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 Toda Jezus mu je rekel: »Juda, s poljubom izdajaš Sina človekovega?«
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 Ko so ti, ki so bili okoli njega, videli, kaj bo sledilo, so mu rekli: »Gospod ali naj udarimo z mečem?«
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 In eden izmed njih je udaril služabnika vélikega duhovnika ter mu odsekal desno uho.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 In Jezus je odgovoril ter rekel: »Pustite do tod.« In dotaknil se je njegovega ušesa ter ga ozdravil.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 Potem je Jezus rekel visokim duhovnikom in tempeljskim stotnikom ter starešinam, ki so prišli k njemu: »Ali ste prišli ven, kakor proti tatu, z meči in palicami?
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 Ko sem bil vsak dan z vami v templju, zoper mene niste iztegnili rok, toda to je vaša ura in oblast teme.«
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 Potem so ga vzeli in ga odvedli ter ga privedli v hišo vélikega duhovnika. Peter pa je sledil od daleč.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 In ko so sredi dvorane prižgali ogenj ter skupaj sedli, je Peter sédel mednje.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 Toda zagledala ga je neka služkinja, ko je sedel poleg ognja in ga tehtno pogledala ter rekla: »Tudi ta človek je bil z njim.«
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 On pa ga je zanikal, rekoč: »Ženska, ne poznam ga.«
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 In malo za tem ga je opazil drug ter rekel: »Tudi ti si izmed njih.« Peter pa je rekel: »Človek, nisem.«
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 In približno eno uro kasneje je še en prepričano potrdil, rekoč: »Resnično, tudi ta je bil z njim, kajti Galilejec je.«
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 Peter pa je rekel: »Človek, ne vem kaj praviš.« In takoj, medtem ko je še govoril, je petelin zapel.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 Gospod pa se je obrnil in pogledal na Petra. In Peter se je spomnil Gospodove besede, kako mu je rekel: »Preden petelin zapoje, me boš trikrat zatajil.«
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 In Peter je odšel ven ter se bridko zjokal.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 Možje, ki so prijeli Jezusa, so ga zasmehovali in ga udarjali.
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 In ko so mu zavezali oči, so ga udarili po obrazu in ga vprašali, rekoč: »Prerokuj, kdo je ta, ki te je udaril?«
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 In mnogo drugih stvari so bogokletno govorili zoper njega.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 In takoj, ko je bil dan, so prišli skupaj starešine izmed ljudi, visoki duhovniki ter pisarji in ga odvedli v svoj véliki zbor, rekoč:
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 »Ali si ti Kristus? Povej nam.« On pa jim je rekel: »Če vam povem, ne boste verjeli
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 in tudi če vas vprašam, mi ne boste odgovorili niti mi [ne boste] pustili oditi.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 Odslej bo Sin človekov sedel na desnici Božje moči.«
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 Potem so vsi rekli: »Ali si ti potem Božji Sin?« On pa jim je rekel: »Vi pravite, da sem.«
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 Rekli so: »Kaj potrebujemo kakršnihkoli nadaljnjih prič? Kajti sami smo slišali iz njegovih lastnih ust.«
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”

< Luka 22 >