< 3 Mojzes 1 >

1 Gospod je zaklical k Mojzesu in mu spregovoril iz šotorskega svetišča skupnosti, rekoč:
Ubangiji ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin Tentin Sujada ya ce,
2 »Spregovori Izraelovim otrokom in jim reci: ›Če katerikoli človek izmed vas prinese dar Gospodu, boste prinesli svojo daritev izmed živine, od tropa in od črede.
“Yi magana da Isra’ilawa ka ce musu, ‘Duk sa’ad da waninku ya kawo hadaya ga Ubangiji, ku kawo hadayarku ta dabba daga garkenku ta shanu ko kuwa daga tumakinku.
3 Če bo njegov dar žgalna daritev od črede, naj daruje samca brez pomanjkljivosti. Daroval ga bo iz svoje lastne prostovoljne volje pri vratih šotorskega svetišča skupnosti pred Gospodom.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga shanu ne, sai yă miƙa namiji marar lahani. Dole yă kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă zama yardajje ga Ubangiji.
4 Svojo roko bo položil na glavo žgalne daritve in ta bo sprejeta zanj, da opravi spravo zanj.
Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya ta ƙonawar, za a kuwa karɓa a madadinsa don a yi kafara dominsa.
5 Bikca bo zaklal pred Gospodom in duhovniki, Aronovi sinovi, bodo prinesli kri in kri poškropili naokoli nad oltarjem, ki je pri vratih šotorskega svetišča skupnosti.
Zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji, Haruna kuwa da’ya’yansa maza firist, za su kawo jinin su kuma yafa shi a kan bagaden a kowane gefe a mashigin Tentin Sujada.
6 Žgalno daritev bo odrl in jo razrezal na koščke.
Zai feɗe hadaya ta ƙonawar, yă yayyanka shi gunduwa-gunduwa.
7 Sinovi duhovnika Arona bodo na oltar položili ogenj in po vrsti na ogenj položili les.
’Ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su hura wuta a bagade, su kuma shirya itace a kan wutar.
8 Duhovniki, Aronovi sinovi, bodo položili dele, glavo in tolščo, po vrsti na les, ki je na ognju, ki je na oltarju,
Sa’an nan’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su shirya gunduwa-gunduwar haɗe da kan da kuma kitsen a kan itace mai cin wuta wanda yake a kan bagaden.
9 toda njegovo drobovino in njegove noge bo umil v vodi. Duhovnik bo vse sežgal na oltarju, da bo žgalna daritev, ognjena daritev, prijetnega vonja Gospodu.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
10 Če bo njegov dar za žgalno daritev od tropov, namreč od ovc ali od koz, bo privedel samca brez pomanjkljivosti.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga garke ne, ko na tumaki, ko na awaki, zai miƙa namiji ne marar lahani.
11 Zaklal ga bo na severni strani oltarja pred Gospodom. Duhovniki, Aronovi sinovi, bodo njegovo kri poškropili naokoli nad oltarjem.
Zai yanka shi a gefen arewa na bagaden a gaban Ubangiji,’ya’yan Haruna firistoci kuwa za su yayyafa jinin dabbar a bagaden a kowane gefe.
12 Razrezal ga bo na koščke, z njegovo glavo in njegovo tolščo. Duhovnik jih bo po vrsti položil na les, ki je na ognju, ki je na oltarju,
Zai yanka shi gunduwa-gunduwa, firist kuwa zai shirya su haɗe da kan, da kuma kitsen a kan itace mai cin wutar da yake a kan bagade.
13 toda drobovje in noge bo umil z vodo. Duhovnik bo vse to prinesel in to sežgal na oltarju. To je žgalna daritev, ognjena daritev, prijetnega vonja Gospodu.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 Če bo žgalna daritev za njegov dar Gospodu od perjadi, potem bo svojo daritev prinesel od grlic ali od mladih golobov.
“‘In hadaya ga Ubangiji ɗin, hadaya ta ƙonawa ta tsuntsaye ce, zai miƙa kurciya ko’yar tattabara.
15 Duhovnik bo to prinesel na oltar in ji odščipnil vrat in jo sežgal na oltarju; in njena kri bo iztisnjena ob strani oltarja.
Firist zai kawo ta bagade, yă murɗe wuyan tsuntsun yă ƙone shi a kan bagade; zai tsiyaye jininsa tsuntsun a gefen bagaden.
16 Njeno golšo bo odtrgal z njenimi peresi in jo odvrgel na vzhodnem delu, poleg oltarja, ob kraju za pepel
Amma zai ɗauki kayan cikin tsuntsun da gashin yă zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka.
17 in nalomi jo s perutmi, toda ne bo je ločil narazen. Duhovnik bo to sežgal na oltarju, na lesu, ki je na ognju. To je žgalna daritev, ognjena daritev, prijetnega vonja Gospodu.‹«
Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, yă ƙone shi. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

< 3 Mojzes 1 >