< Žalostinke 5 >
1 Spomni se, oh Gospod, kaj je prišlo nad nas. Preudari in poglej našo grajo.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Naša dediščina je obrnjena k tujcem, naše hiše k neznancem.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Sirote smo in brez očeta, naše matere so kakor vdove.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Svojo vodo smo pili za denar; naš les nam je prodan.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Naši vratovi so pod preganjanjem. Trudimo se, pa nimamo počitka.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Roko smo izročili k Egipčanom in k Asircem, da bi bili nasičeni s kruhom.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Naši očetje so grešili in jih ni in mi smo nosili njihove krivičnosti.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Služabniki so vladali nad nami. Nikogar ni, da bi nas osvobodil iz njihove roke.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Svoj kruh smo prinašali z nevarnostjo za svoja življenja, zaradi meča iz divjine.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Naša koža je bila črna kakor peč zaradi strašne lakote.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Posiljevali so ženske na Sionu in device v Judovih mestih.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Z njihovo roko so obesili prince. Obrazi starešin niso bili spoštovani.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Zajeli so mladeniče, da meljejo in otroci so padali pod lesom.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Starešine so odšli od velikih vrat, mladeniči od svoje glasbe.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Veselje našega srca je prenehalo, naš ples je obrnjen v žalovanje.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Krona je padla iz naše glave. Gorje nam, da smo grešili!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Zaradi tega peša naše srce, zaradi teh stvari so zatemnjene naše oči.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Zaradi gore Sion, ki je zapuščena, lisice hodijo po njej.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Ti, oh Gospod, ostajaš na veke, tvoj prestol od roda do roda.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Zakaj nas pozabljaš na veke in nas zapuščaš za tako dolgo?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Obrni nas k sebi, oh Gospod in mi bomo obrnjeni; obnovi naše dni kakor od davnine.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Toda popolnoma si nas zavrgel. Zelo si ogorčen zoper nas.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.