< Sodniki 10 >

1 Za Abimélehom je vstal Tolá, sin Puvája, sinú Dodója, mož iz Isahárja, da brani Izrael. Prebival je v Šamíru, na gori Efrájim.
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 Izraelu je sodil triindvajset let in umrl ter bil pokopan v Šamíru.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 Za njim je vstal Gileádec Jaír in Izraelu sodil dvaindvajset let.
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 Imel je trideset sinov, ki so jahali na tridesetih osličjih žrebetih in imeli so trideset mest, ki se imenujejo Havot Jaír do tega dne, ki so v deželi Gileád.
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 Jaír je umrl in bil pokopan v Kamónu.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 Izraelovi otroci pa so v Gospodovih očeh ponovno počeli zlo in služili Báalom, Astarti, bogovom Sirije, bogovom Sidóna, bogovom Moába, bogovom Amónovih otrok in bogovom Filistejcev in zapustili so Gospoda in mu niso služili.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 Gospodova jeza je bila vroča zoper Izrael in prodal jih je v roke Filistejcev in v roke Amónovih otrok.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 Tisto leto so tlačili in zatirali Izraelove otroke; osemnajst let, vse Izraelove otroke, ki so bili na drugi strani Jordana, v deželi Amoréjcev, ki je v Gileádu.
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 Poleg tega so Amónovi otroci prečkali Jordan, da se borijo tudi zoper Juda, zoper Benjamina in zoper Efrájimovo hišo, tako, da je bil Izrael silno stiskan.
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 Izraelovi otroci so vpili h Gospodu, rekoč: »Grešili smo zoper tebe, zato ker smo zapustili svojega Boga in služili tudi Báalom.«
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 Gospod je Izraelovim otrokom rekel: » Mar vas nisem osvobodil pred Egipčani in pred Amoréjci, pred Amónovimi otroki in pred Filistejci?
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 Tudi Sidónci, Amalečani in Maonci so vas zatirali in klicali ste k meni in osvobodil sem vas iz njihove roke.
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 Vendar ste me zapustili in služili drugim bogovom, zato vas ne bom več osvobajal.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Pojdite in jokajte k bogovom, ki ste jih izbrali. Naj vas oni osvobodijo v času vaše stiske.«
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 Izraelovi otroci so rekli Gospodu: »Grešili smo. Stôri nam, karkoli se ti zdi dobro. Prosimo te, samo osvobodi nas ta dan.«
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 Izmed sebe so odstranili tuje bogove in služili Gospodu. Njegova duša je bila užaloščena zaradi Izraelove bede.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 Potem so bili Amónovi otroci zbrani skupaj in se utaborili v Gileádu. Izraelovi otroci pa so se zbrali skupaj in se utaborili v Micpi.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 Ljudstvo in gileádski princi so drug drugemu rekli: »Kateri mož je ta, ki se bo začel boriti zoper Amónove otroke? Ta bo poglavar nad vsemi prebivalci Gileáda.«
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”

< Sodniki 10 >