< Jona 4 >
1 Toda to je Jona silno razžalilo in bil je zelo jezen.
Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
2 Molil je h Gospodu ter rekel: »Prosim te, oh Gospod, ali ni bila to moja beseda, ko sem bil še v svoji deželi? Zatorej sem prej pobegnil v Taršíš, kajti vedel sem, da si milostljiv Bog in usmiljen, počasen za jezo in zelo prijazen in se kesaš zlega.
Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
3 Zatorej sedaj, oh Gospod, vzemi, rotim te, moje življenje od mene, kajti zame je bolje, da umrem, kakor da živim.«
Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
4 Potem je Gospod rekel: »Delaš pravilno, da si jezen?«
Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
5 Tako je Jona odšel ven iz mesta in se usedel na vzhodni strani mesta in si tam postavil šotor in sedèl pod njim v senco, toliko časa, da lahko vidi kaj bo iz mesta nastalo.
Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
6 Gospod Bog pa je pripravil bučo in ji storil, da vzklije nad Jona, da bi bila ta lahko senca nad njegovo glavo, da ga osvobodi pred njegovo žalostjo. Tako je bil Jona buče silno vesel.
Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
7 Toda ko je naslednjega dne vstalo jutro, je Bog pripravil ličinko in ta je napadla bučo, da je ovenela.
Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
8 Ko je sonce vstalo, se je pripetilo, da je Bog pripravil silovit vzhodnik. Sonce je udarjalo na Jonovo glavo, da je slabel in si v sebi želel, da umre ter rekel: »Zame je boljše, da umrem, kakor da živim.«
Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
9 Bog je Jonu rekel: »Delaš pravilno, da si jezen zaradi buče?« Ta je rekel: »Pravilno delam, da sem jezen, celó do smrti.«
Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
10 Potem je Gospod rekel: »Usmiljenje imaš za bučo, za katero nisi delal niti ji storil, da zraste, ki je v [eni] noči vzklila in v [eni] noči propadla,
Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
11 jaz pa naj ne bi prizanesel Ninivam, temu velikemu mestu, v katerem je več kot sto dvajset tisoč oseb, ki ne morejo razlikovati med svojo desnico in svojo levico in tudi veliko živine?«
Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”