< Jona 2 >
1 Potem je Jona iz ribjega trebuha molil h Gospodu, svojemu Bogu
Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
2 in rekel: »Zaradi razloga svoje stiske sem klical h Gospodu in me je slišal. Ven iz trebuha pekla sem klical in ti si slišal moj glas. (Sheol )
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol )
3 Kajti vrgel si me v globino, v sredo morij, in poplave so me obkrožile. Vsi tvoji veliki valovi in tvoji valovi so me preleteli.«
Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
4 Potem sem rekel: »Vržen sem iz tvojega pogleda, vendar bom ponovno gledal k tvojemu svetemu templju.
Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
5 Vode so me obkrožile, celó do duše, globine so me zaprle naokoli, plevel je bil zavit okoli moje glave.
Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
6 Odšel sem navzdol, k vznožjem gora. Zemlja, s svojimi zapahi, je bila okoli mene na veke, vendar si ti moje življenje privedel gor iz trohnenja, oh Gospod, moj Bog.
Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
7 Ko je moja duša slabela znotraj mene, sem se spomnil Gospoda. Moja molitev je vstopila k tebi, v tvoj sveti tempelj.
“Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
8 Tisti, ki obeležujejo lažnive ničevosti, zapuščajo svoje lastno usmiljenje.
“Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
9 Toda jaz ti bom žrtvoval z glasom zahvaljevanja; plačal bom to, kar sem se zaobljubil. Rešitev duš je od Gospoda.«
Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
10 In Gospod je spregovoril ribi in izbljuvala je Jona na kopno zemljo.
Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.