< Joel 1 >

1 Gospodova beseda, ki je prišla Joélu, Petuélovemu sinu.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Poslušajte to, vi starci in pazljivo prisluhnite, vsi vi prebivalci dežele. Ali je bilo to v vaših dneh ali celo v dneh vaših očetov?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Pripovedujte svojim otrokom o tem in naj vaši otroci pripovedujejo svojim otrokom in njihovi otroci naslednjemu rodu.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 To, kar je kosmata gosenica pustila, je pojedla leteča kobilica; in to, kar je leteča kobilica pustila, je pojedla škodljiva gosenica; in to, kar je pustila škodljiva gosenica, je pojedla gosenica.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Prebudite se, vi pijanci in jokajte, tulite vsi vi vinski pivci zaradi novega vina, kajti odrezan je od vaših ust.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Kajti narod je prišel nad mojo deželo, močan in brezštevilen, katerih zobje so zobje leva in ima kočnike velikega leva.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 Opustošil je mojo trto in olupil moje figovo drevo. Naredil ga je razgaljenega in ga vrgel proč; njegove mladike so pobeljene.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Žalujte kakor devica, opasana z vrečevino za soprogom svoje mladosti.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Jedilna daritev in pitna daritev je odrezana od Gospodove hiše. Duhovniki, Gospodovi služabniki, žalujejo.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Polje je opustošeno, zemlja žaluje, kajti žito je opustošeno. Novo vino je posušeno, olje peša.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Bodite osramočeni, oh vi poljedelci. Tulite, oh vi obrezovalci trte, zaradi pšenice in zaradi ječmena, ker je žetev polja propadla.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 Trta je posušena in figovo drevo peša. Granatovec, tudi palmovo drevo in jablana, celó vsa poljska drevesa so ovenela, ker je veselje zamrlo pred človeškimi sinovi.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Opašite se in objokujte, vi duhovniki; tulite, služabniki oltarja, pridite, vso noč ležite v vrečevini, vi služabniki mojega Boga, kajti jedilna daritev in pitna daritev je zadržana pred hišo vašega Boga.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Posvetite post, skličite slovesen zbor, zberite starešine in vse prebivalce dežele v hišo Gospoda, svojega Boga in kličite h Gospodu:
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 »Gorje zaradi dneva!« Kajti dan Gospodov je pri roki in to bo prišlo kakor uničenje od Vsemogočnega.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Mar ni hrana odrezana izpred naših oči, da, radost in veselje od hiše našega Boga?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Seme je razpadlo pod njihovimi grudami, kašče ležijo zapuščene, skednji so razpadli, kajti žito je ovenelo.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Kako stokajo živali! Živine črede so zmedene, ker nimajo pašnika; da, tropi ovac so zapuščeni.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Oh Gospod, k tebi bom klical, kajti ogenj je požrl pašnike divjine in plamen je požgal vsa poljska drevesa.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Tudi poljske živali kličejo k tebi, kajti reke vodá so posušene in ogenj je pogoltnil pašnike divjine.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joel 1 >