< Jeremija 4 >

1 »Če se hočeš vrniti, oh Izrael, « govori Gospod, »se vrni k meni. Če hočeš odstraniti svoje ogabnosti izpred mojega pogleda, potem ne boš odtaval.
“In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
2 Prisegel boš: › Gospod živi v resnici in sodbi in v pravičnosti‹« in narodi se bodo blagoslavljali v njem in v njem bodo slavili.
kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
3 Kajti tako govori Gospod Judovim možem in Jeruzalemu: »Pobranajte svoja neposejana tla in ne sejte med trnjem.
Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
4 Obrežite se Gospodu in odstranite prednje kožice svojega srca, vi, Judovi možje in prebivalci Jeruzalema, da ne bi moja razjarjenost prišla kakor ogenj in tako požgala, da nihče ne more pogasiti – zaradi hudobije vaših ravnanj.
Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
5 Razglasite v Judu in objavite v [prestolnici] Jeruzalem in recite: ›Zatrobite na šofar v deželi.‹ Kličite, zberite se skupaj in recite: ›Zberite se skupaj in pojdimo v obrambna mesta.‹
“Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
6 Postavite prapor proti Sionu. Umaknite se, ne ostanite, kajti jaz bom privedel hudo iz severa in veliko uničenje.
Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
7 Lev je prišel iz svoje goščave in uničevalec poganov je na svoji poti; odšel je iz svojega kraja, da tvojo deželo naredi zapuščeno in tvoja mesta bodo opustošena, brez prebivalca.
Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
8 Zaradi tega se opašite z vrečevino, žalujte in tulite, kajti kruta Gospodova jeza ni odvrnjena od nas.
Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
9 Zgodilo se bo na ta dan, « govori Gospod, » da bo srce kralja in srce princev oslabelo in duhovniki bodo osupli in preroki se bodo spraševali.«
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
10 Potem sem rekel: »Ah, Gospod Bog! Zagotovo si zelo prevaral to ljudstvo in Jeruzalem, rekoč: ›Imeli boste mir, ‹ medtem ko meč sega do duše.«
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
11 Ob tistem času bo rečeno temu ljudstvu in [prestolnici] Jeruzalem: »Suh veter visokih krajev v divjini proti hčeri mojega ljudstva, ne da preveja niti da očisti,
A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
12 celó poln veter iz tistih krajev bo prišel k meni. Sedaj bom tudi jaz izrekel obsodbo zoper njih.«
iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
13 Glej, prišel bo gor kakor oblaki in njegovi bojni vozovi bodo kakor vrtinčast veter. Njegovi konji so bolj nagli kakor orli. Gorje nam! Kajti oplenjeni smo.
Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
14 »Oh [prestolnica] Jeruzalem, umij svoje srce pred zlobnostjo, da boš lahko rešena. Doklej bodo tvoje prazne misli prenočevale znotraj tebe?
Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
15 Kajti glas razglaša od Dana in objavlja stisko od gore Efrájim.
Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
16 Dajte omenjati narodom, glejte, objavite zoper [prestolnico] Jeruzalem, da stražarji prihajajo iz daljne dežele in objavite njihov glas zoper Judova mesta.
“A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
17 Kakor čuvaji polja so oni zoper njo vsenaokrog, zato ker je bila uporna zoper mene, « govori Gospod.
Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
18 »Tvoja pot in tvoja početja so ti povzročila te stvari; to je tvoja zlobnost, ker je ta grenka, ker ta sega v tvoje srce.
“Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
19 Moja notranjost, moja notranjost! Zaskrbljen sem prav v svojem srcu; moje srce dela v meni hrup; ne morem ohraniti miru, ker si slišala, oh moja duša, zvok šofarja, alarm vojne.
Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
20 Uničenje na uničenje je razkričano, kajti celotna dežela je oplenjena. Moji šotori so nenadoma oplenjeni in moje zavese v trenutku.
Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
21 Doklej bom videl prapor in slišal zvok šofarja?
Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
22 Kajti moje ljudstvo je nespametno, niso me spoznali; neumni otroci so in nobenega razumevanja nimajo. Modri so, da počno hudo, toda za početje dobrega nimajo spoznanja.«
“Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
23 Pogledal sem zemljo in glej, ta je bila brez oblike ter prazna; in [na] nebo, pa ni imelo nobene svetlobe.
Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
24 Pogledal sem gore in glej, trepetale so in vsi hribi so se rahlo gibali.
Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
25 Pogledal sem in glej, tam ni bilo nobenega človeka in vse nebeške ptice so odletele.
Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
26 Pogledal sem in glej, rodoviten kraj je bila divjina in vsa njegova mesta so bila zrušena ob Gospodovi prisotnosti in z njegovo kruto jezo.
Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
27 Kajti tako je rekel Gospod: »Celotna dežela bo zapuščena, vendar ne bom naredil popolnega konca.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
28 Zaradi tega bo zemlja žalovala in nebo nad [njo] bo črno. Ker sem to govoril, sem to namenil in se ne bom kesal niti se ne bom obrnil nazaj od tega.«
Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
29 Celotno mesto bo pobegnilo zaradi zvoka konjenikov in lokostrelcev; šli bodo v goščave in plezali na skale. Vsako mesto bo zapuščeno in ni človeka, da tam prebiva.
Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
30 Ko si oplenjena, kaj boš storila? Čeprav se oblačiš s temno rdečo, čeprav se krasiš z ornamenti iz zlata, čeprav si obrobljaš svoj obraz z ličenjem, se boš zaman naredila lepo; tvoji ljubimci te bodo prezirali, stregli ti bodo po življenju.
Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
31 Kajti slišal sem glas ženske kakor v porodnih bolečinah in tesnobo kakor od tiste, ki rojeva svojega prvega otroka, glas sionske hčere, ki se objokuje, ki razširja svoji roki, rekoč: »Gorje mi sedaj! Kajti moja duša je izmučena zaradi morilcev.«
Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”

< Jeremija 4 >