< Jeremija 29 >

1 Torej to so besede pisma, ki ga je prerok Jeremija poslal iz Jeruzalema preostanku starešin, ki so bili odvedeni ujeti, duhovnikom, prerokom in vsem ljudstvu, ki jih je Nebukadnezar ujete odvedel iz Jeruzalema v Babilon
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 (potem so bili kralj Jehoníja, kraljica, evnuhi, princi iz Juda in Jeruzalema ter tesarji in kovači odvedeni iz Jeruzalema)
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 po roki Šafánovega sina Elasá in Hilkijájevega sina Gemarjá (katera je Judov kralj Sedekíja poslal v Babilon k babilonskemu kralju Nebukadnezarju), rekoč:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 »Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog, vsem, ki so odvedeni ujeti, ki sem jim povzročil, da so odvedeni proč iz Jeruzalema v Babilon:
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 ›Zgradite si hiše in prebivajte v njih, zasajajte vrtove in jejte njihov sad,
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 jemljite si žene in zaplodite sinove ter hčere, in vzemite žene za svoje sinove in svoje hčere dajte soprogom, da bodo lahko rodile sinove in hčere, da boste tam lahko povečani in ne zmanjšani.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Iščite mir mestu, kamor sem vam povzročil, da ste bili odvedeni ujeti in zanj molite h Gospodu, kajti v njegovem miru boste vi imeli mir.‹
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 Kajti tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: »Naj vas vaši preroki in vaši vedeževalci, ki so v vaši sredi, ne zavajajo, niti ne prisluhnite svojim sanjam, ki ste jim povzročili, da so sanjane.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 Kajti lažno vam prerokujejo v mojem imenu. Nisem jih poslal, « govori Gospod.
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 Kajti tako govori Gospod: »Da vas bom po tem, ko bo v Babilonu dovršenih sedemdeset let, obiskal in izvêdel svojo dobro besedo napram vam, v tem, da povzročim, da se vrnete na ta kraj.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 Kajti poznam misli, ki jih mislim napram vam, « govori Gospod, »misli miru in ne zla, da vam dam pričakovan konec.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Takrat boste klicali k meni in boste šli in molili k meni in vam bom prisluhnil.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 Iskali me boste in me našli, ko me boste iskali z vsem svojim srcem.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 Dal se vam bom najti, « govori Gospod, »in vaše ujetništvo bom odvrnil proč in zbral vas bom izmed vseh narodov in iz vseh krajev, kamor sem vas pregnal, « govori Gospod, »in jaz vas bom ponovno privedel na kraj, od koder sem vam povzročil, da ste bili odvedeni ujeti.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Ker ste rekli: › Gospod nam je v Babilonu vzdignil preroke; ‹
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 vedite, da tako govori Gospod o kralju, ki sedi na Davidovem prestolu in o vsemu ljudstvu, ki prebiva v tem mestu in o vaših bratih, ki niso šli z vami naprej v ujetništvo; «
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 tako govori Gospod nad bojevniki: »Poglejte, nadnje bom poslal meč, lakoto in kužno bolezen in naredil jih bom kot ogabne fige, ki se ne morejo pojesti, ker so tako zle.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 Preganjal jih bom z mečem, z lakoto in s kužno boleznijo in izročil jih bom, da bodo odstranjeni k vsem kraljestvom zemlje, da bodo prekletstvo, osuplost, posmeh in graja med vsemi narodi, kamor sem jih pregnal,
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 ker niso prisluhnili mojim besedam, « govori Gospod, »ki sem jim jih pošiljal po svojih služabnikih prerokih, jih zgodaj vzdigoval in pošiljal; toda vi niste hoteli poslušati, « govori Gospod.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 »Poslušajte torej besedo od Gospoda, vsi vi iz ujetništva, ki sem vas poslal iz Jeruzalema v Babilon.
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog o Kolajájevemu sinu Ahábu, in o Maasejájevemu sinu Sedekíju, ki vam prerokujeta laž v mojem imenu: ›Glejte, izročil ju bom v roko babilonskega kralja Nebukadnezarja in ta ju bo ubil pred vašimi očmi.‹
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 Od njiju bo vse Judovo ujetništvo, ki je v Babilonu, povzelo prekletstvo, rekoč: › Gospod naj ti stori kakor Sedekíju in kakor Ahábu, ki ju je babilonski kralj pekel na ognju, (questioned)
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 ker sta zagrešila podlost v Izraelu in zagrešila zakonolomstvo z ženami svojih sosedov in v mojem imenu govorila lažnive besede, ki jima jih nisem zapovedal. Celo vedel sem in sem priča, ‹ govori Gospod.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 › Tako boš tudi ti govoril Šemajáju Nehelaméjcu, rekoč:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 ›Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog, rekoč: ›Ker si v svojem imenu poslal pisma vsemu ljudstvu, ki so v Jeruzalemu in k duhovniku Cefanjáju, Maasejájevemu sinu in vsem duhovnikom, rekoč:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 › Gospod te je postavil za duhovnika namesto duhovnika Jojadája, da bi bili častniki v Gospodovi hiši, za vsakega človeka, ki je zmešan in se dela preroka, da ga bi vtaknil v ječo in v klade.
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 Zdaj torej, zakaj nisi grajal Jeremija iz Anatóta, ki se vam dela prerok?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 Kajti zato je poslal k nam v Babilon, rekoč: ›To ujetništvo je dolgo. Zgradite si hiše in prebivajte v njih, zasadite vrtove in jejte sad od njih.‹«
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Duhovnik Cefanjá je to pismo prebral v ušesa preroka Jeremija.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Potem je prišla Gospodova beseda Jeremiju, rekoč:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 »Pošlji k vsem tem iz ujetništva, rekoč: ›Tako govori Gospod glede Šemajája Nehelaméjca: ›Zato, ker je ta Šemajá prerokoval zoper vas, pa ga nisem poslal jaz in vam je storil, da zaupate v laž,
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 zato tako govori Gospod: ›Glejte, kaznoval bom Šemajája Nehelaméjca in njegovo seme. Ne bo imel človeka, da prebiva med tem ljudstvom; niti ne bo gledal dobrega, ki ga bom storil za svoje ljudstvo, ‹ govori Gospod; ›ker je učil upor zoper Gospoda.‹«
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremija 29 >