< Jeremija 28 >

1 Pripetilo se je isto leto, v začetku kraljevanja Judovega kralja Sedekíja, v četrtem letu in v petem mesecu, da mi je spregovoril Hananjá, sin preroka Azúrja, ki je bil iz Gibeóna, v Gospodovi hiši, v prisotnosti duhovnikov in vsega ljudstva, rekoč:
A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
2 »Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog, rekoč: ›Zlomil sem jarem babilonskega kralja.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
3 V dveh letih bom ponovno na ta kraj privedel vse posode Gospodove hiše, ki jih je babilonski kralj Nebukadnezar vzel iz tega kraja in jih odnesel v Babilon.
Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
4 Ponovno bom na ta kraj privedel Jehoníja, sina Jojakíma, Judovega kralja, z vsemi Judovimi ujetniki, ki so šli v Babilon, ‹ govori Gospod, ›kajti jaz bom zlomil jarem babilonskega kralja.‹«
Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
5 Potem je prerok Jeremija rekel preroku Hananjáju, v prisotnosti duhovnikov in v prisotnosti vsega ljudstva, ki je stalo v Gospodovi hiši,
Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
6 celo prerok Jeremija je rekel: »Amen. Gospod naj tako stori. Gospod naj izpolni tvoje besede, ki si jih prerokoval, da ponovno privede posode Gospodove hiše in vse, kar je odvedeno ujeto, iz Babilona na ta kraj.
Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
7 Kljub temu poslušaj sedaj te besede, ki jih govorim v tvoja ušesa in v ušesa vsega ljudstva.
Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
8 Preroki, ki so bili pred menoj in pred teboj od davnine, so prerokovali tako zoper mnoge dežele kakor zoper velika kraljestva, o vojni in o zlu in o kužni bolezni.
Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
9 Prerok, ki prerokuje o miru, ko se bo zgodila prerokova beseda, potem bo prerok znan, da ga je resnično poslal Gospod.«
Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
10 Potem je prerok Hananjá snel jarem iz vratu preroka Jeremija in ga zlomil.
Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
11 Hananjá je spregovoril v prisotnosti vsega ljudstva, rekoč: »Tako govori Gospod: ›Celo tako bom zlomil jarem babilonskega kralja Nebukadnezarja iz vratu vseh narodov, v času dveh polnih let.‹« In prerok Jeremija je odšel svojo pot.
ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
12 Potem je Gospodova beseda prišla preroku Jeremiju, potem ko je prerok Hananjá zlomil jarem iz vratu preroka Jeremija, rekoč:
Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 »Pojdi in povej Hananjáju, rekoč: ›Tako govori Gospod: ›Zlomil si lesene jarme, toda zanje boš naredil železne jarme.‹
“Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
14 Kajti tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: ›Železen jarem sem položil na vrat vseh teh narodov, da bodo lahko služili babilonskemu kralju Nebukadnezarju; in služili mu bodo in dal sem mu tudi poljske živali.‹«
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
15 Potem je prerok Jeremija rekel preroku Hananjáju: »Prisluhni sedaj Hananjá: › Gospod te ni poslal, temveč ti zavajaš to ljudstvo, da zaupa v laž.‹
Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
16 Zato tako govori Gospod: ›Glej, vrgel te bom iz obličja zemlje. To leto boš umrl, ker si učil upor zoper Gospoda.‹«
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
17 Tako je prerok Hananjá to isto leto umrl, v sedmem mesecu.
A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

< Jeremija 28 >