< Jeremija 18 >
1 Beseda, ki je prišla Jeremiju od Gospoda, rekoč:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 »Vstani in pojdi dol k lončarjevi hiši in tam ti bom povzročil, da boš slišal moje besede.«
“Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
3 Potem sem odšel dol k lončarjevi hiši in glej, izdeloval je delo na kolesih.
Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
4 Posoda, ki jo je naredil iz ila je bila iznakažena v lončarjevi roki. Tako je še enkrat naredil drugo posodo, kakor se je lončarju zdelo dobro, da jo naredi.
Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
5 Potem je k meni prišla Gospodova beseda, rekoč:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
6 »Oh Izraelova hiša, mar ne morem narediti z vami kakor ta lončar?« govori Gospod. »Glejte, kakor je ilo v lončarjevi roki, tako ste vi v moji roki, oh Izraelova hiša.
“Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
7 V kakšnem trenutku bom govoril glede naroda in glede kraljestva, da ga izruvam, poderem in uničim.
A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
8 Če [pa] se ta narod, zoper katerega sem proglasil, obrne od svojega zla, se bom pokesal od zla, ki sem jim ga mislil storiti.
in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
9 V kakšnem trenutku bom govoril glede naroda in glede kraljestva, da ga zgradim in zasadim.
In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
10 Če [pa] dela zlo v mojem pogledu, da ne uboga mojega glasu, potem se bom pokesal dobrega, s katerim sem rekel, da bi jim koristil.
in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
11 Zdaj torej pojdi, govori Judovim možem in prebivalcem Jeruzalema, rekoč: ›Tako govori Gospod; ›Glejte, zoper vas oblikujem zlo in zoper vas naklepam naklep. Torej se vrnite, vsakdo iz svoje hudobne poti in naredite svoje poti in svoja dejanja dobra.‹«
“Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
12 Rekli so: »Tam ni nobenega upanja, temveč bomo hodili po svojih lastnih naklepih in vsakdo izmed nas bo počel zamisel svojega zlega srca.«
Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
13 Zato tako govori Gospod: »Vprašajte torej med pogani, kdo je slišal takšne stvari. Izraelova devica je storila zelo strašno stvar.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
14 Mar bo človek zapustil libanonski sneg, ki prihaja iz poljske skale? Mar bodo hladne tekoče vode, ki prihajajo iz drugega kraja, zapuščene?
Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
15 Ker me je moje ljudstvo pozabilo so zažigali kadilo ničnostim in le-ti so jim storili, da se spotikajo na svojih poteh od starodavnih steza, da hodijo po stezah, na poti, ki ni nasuta,
Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
16 da naredijo svojo deželo zapuščeno in neprestan posmeh; vsak, kdor gre tam mimo, bo osupel in bo zmajeval z glavo.
Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
17 Pred sovražnikom jih bom razkropil kakor z vzhodnim vetrom; pokazal jim bom hrbet in ne obraza, na dan njihove katastrofe.«
Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
18 Potem so rekli: »Pridite in naklepajmo naklepe zoper Jeremija; kajti postava ne bo izginila od duhovnika, niti nasvet od modrega, niti beseda od preroka. Pridite in udarimo ga z jezikom in ne dajmo pozornosti katerikoli izmed njegovih besed.«
Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
19 Nakloni mi pozornost, oh Gospod in prisluhni glasu tistih, ki se pričkajo z menoj.
Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
20 Mar bo zlo poplačilo za dobro? Kajti izkopali so jamo za mojo dušo. Spomni se, da sem stal pred teboj, da govorim dobro zanje in da odvrnem tvoj bes od njih.
Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
21 Zato njihove otroke izroči lakoti in njihovo kri izlij s silo meča; in naj bodo njihove žene oropane svojih otrok in bodo vdove; in naj bodo njihovi možje usmrčeni; naj bodo njihovi mladeniči v bitki umorjeni z mečem.
Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
22 Naj bo krik slišan od njihovih hiš, ko boš nadnje nenadoma privedel krdelo, kajti izkopali so jamo, da bi me ujeli in skrili pasti za moja stopala.
Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
23 Vendar, Gospod, ti poznaš vse njihove namere zoper mene, da me ubijejo. Ne odpusti njihove krivičnosti niti njihovega greha ne izbriši pred svojim pogledom, temveč naj bodo zrušeni pred teboj; tako postopaj z njimi v času svoje jeze.
Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.