< Izaija 62 >

1 Zaradi Siona ne bom molčal in zaradi Jeruzalema ne bom počival, dokler njegova pravičnost ne gre naprej kakor sijaj in njegova rešitev duš kakor svetilka, ki gori.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 Pogani bodo videli tvojo pravičnost in vsi kralji tvojo slavo in imenovana boš z novim imenom, ki ga bodo poimenovala Gospodova usta.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 Krona slave boš v Gospodovi roki in kraljevski diadem v roki svojega Boga.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 Ne boš več imenovana Zapuščena niti ne bo tvoja dežela imenovana Opustošena, temveč se boš imenovala Hefziba in tvoja dežela Beula. Kajti Gospod se razveseljuje v tebi in tvoja dežela bo omožena.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 Kajti kakor mladenič poroči devico, tako se bodo tvoji sinovi poročili s teboj in kakor se ženin razveseljuje nad nevesto, tako se bo tvoj Bog veselil nad teboj.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 Postavil sem stražarje na tvoja obzidja, oh Jeruzalem, ki niti podnevi niti ponoči ne bodo nikoli mirovali. Vi, ki omenjate Gospoda, ne molčite
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 in njemu ne dajajte nobenega počitka, dokler ne osnuje in dokler ne naredi [prestolnice] Jeruzalem [za] hvalo na zemlji.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 Gospod je prisegel pri svoji desnici in pri laktu svoje moči: »Zagotovo ne bom več dajal tvojega žita, da bi bil hrana tvojim sovražnikom in sinovi tujca ne bo pili tvojega vina, za katerega si se trudila,
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 temveč tisti, ki so ga nabrali, ga bodo jedli in hvalili Gospoda in tisti, ki so ga zbrali skupaj, ga bodo pili na dvorih moje svetosti.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Pojdite skozi, pojdite skozi velika vrata, pripravite pot ljudstvu, nasujte, nasujte glavno cesto, poberite kamne, dvignite prapor za ljudstvo.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 Glejte, Gospod je razglasil do konca sveta: »Sionski hčeri recite: ›Glej tvoja rešitev duš prihaja, glej, njegova nagrada je z njim in njegovo delo pred njim.‹«
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 Klicali jih bodo Sveto ljudstvo, Odkupljeni od Gospoda in ti boš imenovana ›Poiskana, ‹ ›Mesto, ki ni zapuščeno.‹
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.

< Izaija 62 >