< Izaija 30 >
1 »Gorje upornim otrokom, « govori Gospod, »ki jemljejo nasvet, toda ne od mene in ki se pokrivajo s pokrivalom, toda ne od mojega duha, da lahko grehu dodajo greh,
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 ki hodijo, da bi šli dol v Egipt, pa niso vprašali pri mojih ustih, da se ojačajo v faraonovi moči in da zaupajo v egiptovsko senco!
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 Zato bo faraonova moč vaša sramota in zaupanje v egiptovsko senco vaša zmeda.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Kajti njegovi princi so bili pri Coanu in njegovi predstavniki so prišli do Hanésa.
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 Vsi so bili osramočeni od ljudstva, ki jim ni moglo koristiti niti jim biti v pomoč niti dobiček, temveč sramota in tudi graja.
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Breme živali juga. V deželo stiske in tesnobe, od koder je prišel mlad in star lev, gad in strupena leteča kača, bodo svoja bogastva odnesli na ramenih mladih oslov in svoje zaklade na kameljih grbah k ljudstvu, ki jim ne bo koristilo.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Kajti Egipčani bodo pomagali v prazno in zaman, zato sem glede tega klical: ›Njihova moč mora prenehati.‹
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Torej pojdite, zapišite to pred njimi na tablo in zabeležite v knjigo, da bo lahko za čas, ki pride na veke vekov,
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 da je to uporno ljudstvo, lažnivi otroci, otroci, ki nočejo poslušati Gospodove postave,
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 ki vidcem pravijo: ›Ne vidite‹ in prerokom: ›Ne prerokujte nam pravilnih stvari, govorite nam laskave stvari, prerokujte prevare.
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 Spravite se iz poti, odvrnite se iz steze, Svetemu Izraelovemu naredite, da odide izpred nas.‹«
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 Zatorej tako govori Sveti Izraelov: »Ker prezirate to besedo in zaupate v zatiranje in perverznost in ostajate na njej,
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 zato vam bo ta krivičnost kakor vrzel, pripravljena, da pade, naraščajoča iz visokega obzidja, katerega zlom pride nenadoma, v trenutku.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 Zlomil ga bo kakor lomljenje lončarjeve posode, ki je zdrobljena na koščke. Ne bo prizanesel, tako da tam, v lomljenju le-tega, ne bo najti črepinje, da bi vzel ogenj iz ognjišča ali da bi s tem zajel vodo iz vrča.
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Kajti tako govori Gospod Bog, Sveti Izraelov: »›V vračanju in počivanju boste rešeni; v spokojnosti in zaupanju bo vaša moč, ‹ pa niste hoteli.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 Temveč ste rekli: ›Ne, kajti bežali bomo na konjih; ‹ zatorej boste bežali. ›Jahali bomo na naglih; ‹ zato bodo tisti, ki vas preganjajo, nagli.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Tisoč jih bo bežalo ob graji enega; ob graji petih boste bežali, dokler ne boste ostali kakor drog na vrhu gore in kakor zastava na hribu.«
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 Zato bo Gospod čakal, da vam bo lahko milostljiv in zato bo povzdignjen, da bo lahko imel usmiljenje do vas, kajti Gospod je Bog sodbe. Blagoslovljeni so vsi tisti, ki čakajo nanj.
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Kajti ljudstvo bo prebivalo na Sionu, pri Jeruzalemu. Ne boš več jokal. Zelo ti bo milostljiv ob glasu tvojega klica; ko ga bo zaslišal, ti bo odgovoril.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Čeprav ti Gospod daje kruh nadloge in vodo stiske, vendar tvoji učitelji ne bodo več odstranjeni v kot, temveč bodo tvoje oči videle tvoje učitelje
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 in tvoja ušesa bodo slišala za teboj besedo, rekoč: »To je pot, po njej hodite, « ko se obrnete k desnici in ko se obrnete k levici.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Omadeževali boste tudi pokrivalo svojih rezanih podob iz srebra in ornament svojih ulitih podob iz zlata. Vrgel jih boš proč kakor menstrualno krpo; temu boš rekel: »Pojdi ven.«
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Potem bo dal dež tvojemu semenu, da boš z njim posejal tla in kruh od donosa zemlje in to bo debelo in obilno. Na ta dan se bo tvoja živina pasla na velikih pašnikih.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Prav tako bodo voli in mladi osli, ki obdelujejo zemljišče, jedli čisto krmo, ki je bila prevejana z lopato in z vejálnikom.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 Tam bodo na vsaki visoki gori in na vsakem visokem hribu reke in potoki vodá, na dan velikega pokola, ko bodo padli stolpi.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Poleg tega bo svetloba lune kakor svetloba sonca in svetloba sonca bo sedemkratna, kakor svetloba sedmih dni, na dan, ko Gospod obveže vrzel svojega ljudstva in ozdravi udarec njihove rane.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Glej, ime Gospoda prihaja od daleč, goreč z njegovo jezo in njegovo breme je težko. Njegove ustnice so polne ogorčenja in njegov jezik kakor požirajoč ogenj.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 Njegov dih bo kakor preplavljajoč vodotok segel do sredine vratu, da narode preseje s sitom ničnosti in tam bo brzda v čeljustih ljudstva, ki jim bo povzročala, da se opotekajo.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Imeli boste pesem, kakor v noči, ko se praznuje sveta slovesnost; in veselje srca, kakor ko gre nekdo s piščaljo, da pride na Gospodovo goro, k Mogočnemu Izraelovemu.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 Gospod bo svojemu veličastnemu glasu povzročil, da bo slišan in pokazal bo spuščanje svojega lakta, z ogorčenjem svoje jeze in s plamenom požirajočega ognja, z razprševanjem, neurjem in zrni toče.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 Kajti preko Gospodovega glasu bo Asirec, ki je udaril s palico, potolčen.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 Na vsakem kraju, kjer bo prešla osnovana palica, ki jo bo Gospod položil nanj, bo to z bobniči in harfami, in v bitkah vihtenja se bo boril z njo.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Kajti Tofet je odrejen od davnine; da, za kralja je pripravljen; naredil ga je globokega in velikega. Njegova grmada je ogenj in veliko lesa. Gospodov dih ga vname kakor tok žvepla.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.