< Izaija 2 >

1 Beseda, ki jo je Izaija, Amócov sin, videl glede Juda in Jeruzalema.
Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
2 Zgodilo se bo v poslednjih dneh, da bo gora Gospodove hiše osnovana na vrhu gora in povišana bo nad hribe. In vsi narodi se bodo stekali k njej.
A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
3 Mnogo ljudstva bo šlo in reklo: »Pridite in pojdimo gor na Gospodovo goro, k hiši Jakobovega Boga. Učil nas bo svojih poti in hodili bomo po njegovih stezah, kajti iz Siona bo izšla postava in Gospodova beseda iz Jeruzalema.«
Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
4 Sodil bo med narodi, oštel bo mnoga ljudstva. Svoje meče bodo prekovali v lemeže in svoje sulice v obrezovalne kavlje. Narod ne bo vzdignil meča zoper narod niti se ne bodo več učili bojevanja.
Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
5 Oh Jakobova hiša, pridite in hodímo v Gospodovi svetlobi.
Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
6 Zatorej si zapustil svoje ljudstvo, Jakobovo hišo, ker so bili izpolnjeni od vzhoda in so napovedovalci usode kakor Filistejci in sebi ugajajo v otrocih tujcev.
Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
7 Njihova dežela je polna srebra in zlata niti tam ni konca njihovih zakladov. Njihova dežela je polna konj niti tam ni konca njihovih bojnih voz.
Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
8 Njihova dežela je polna malikov, obožujejo delo svojih lastnih rok, to, kar so naredili njihovi lastni prsti.
Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
9 Zloben človek se priklanja in velik človek se ponižuje, zato jim ne odpusti.
Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
10 Vstopi v skalo in se skrij v prahu zaradi strahu pred Gospodom in zaradi slave njegovega veličanstva.
Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
11 Človekovi vzvišeni pogledi bodo ponižani in oholost ljudi bo upognjena in sam Gospod bo na ta dan povišan.
Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12 Kajti dan Gospoda nad bojevniki bo nad vsakim, ki je ponosen in vzvišen in nad vsakim, ki je povzdignjen, in ta bo ponižan;
Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
13 in nad vsemi libanonskimi cedrami, ki so visoke in povzdignjene in nad vsemi bašánskimi hrasti
domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
14 in nad vsemi visokimi gorami in nad vsemi hribi, ki so povzdignjeni,
domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
15 in nad vsakim visokim stolpom in nad vsakim utrjenim zidom,
domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
16 in na vseh ladjah iz Taršíša in na vseh prijetnih slikah.
domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
17 Nadutost človeka bo upognjena in oholost ljudi bo ponižana. Samo Gospod bo povišan na ta dan.
Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
18 Malike bo popolnoma odpravil.
za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
19 Šli bodo v skalne luknje in v zemeljske votline zaradi strahu pred Gospodom in zaradi slave njegovega veličanstva, ko se on vzdiguje, da strašno strese zemljo.
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
20 Na tisti dan bo človek vrgel svoje malike iz srebra in svoje malike iz zlata, ki so si jih naredili, vsakdo za oboževanje, krtom in netopirjem,
A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
21 da bo šel v skalne razpoke in na vrhove razdrapanih skal, zaradi strahu pred Gospodom in zaradi slave njegovega veličanstva, ko se bo vzdigoval, da strašno strese zemljo.
Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
22 Odvrnite se od človeka, katerega dih je v njegovih nosnicah, kajti v čem je ta cenjen?
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

< Izaija 2 >