< Ozej 5 >

1 Poslušajte to, oh duhovniki in pazljivo prisluhnite, vi, Izraelova hiša in nagnite uho, oh kraljeva hiša, kajti sodba je zoper vas, ker ste bili zanka na Micpi in mreža, razpeta na [gori] Tabor.
“Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
2 Puntarji so prodorni, da naredijo pokol, čeprav sem bil jaz oštevalec njih vseh.
’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
3 Poznam Efrájima in Izrael ni skrit pred menoj, kajti sedaj, oh Efrájim, zagrešuješ vlačugarstvo in Izrael je omadeževan.«
Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
4 Svojih ravnanj ne bodo snovali, da bi se obrnili k svojemu Bogu, kajti duh vlačugarstev je v njihovi sredi in niso spoznali Gospoda.
“Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
5 Izraelov ponos pričuje v njegov obraz, zatorej bosta Izrael in Efrájim padla v svoji krivičnosti. Tudi Juda bo padel z njima.
Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
6 Šli bodo s svojimi tropi in s svojimi čredami, da bi iskali Gospoda, toda ne bodo ga našli. On se je oddaljil od njih.
Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
7 Zahrbtno so ravnali zoper Gospoda, kajti zaplodili so tuje otroke. Sedaj jih bo požrl mesec z njihovimi deleži.
Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
8 Zatrobite na kornét v Gíbei in na trobento v Rami, kričite glasno pri Bet Avenu, za teboj, oh Benjamin.
“Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
9 Efrájim bo zapuščen na dan oštevanja. Med Izraelovimi rodovi sem dal spoznati tisto, kar zagotovo bo.
Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
10 Judovi princi so bili kakor tisti, ki odstranjujejo mejo, zatorej bom nanje izlil svoj bes kakor vodo.
Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
11 Efrájim je zatiran in razklan na sodbi, zato ker je voljan hodil za [človeško] zapovedjo.
An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
12 »Zato bom Efrájimu kakor molj, Judovi hiši pa kakor gniloba.
Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
13 Ko je Efrájim videl svojo slabost in Juda videl svojo rano, takrat je šel Efrájim k Asircu in poslal h kralju Jarebu in vendar vas on ni mogel ozdraviti niti ozdraviti vaše rane.
“Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
14 Kajti jaz bom Efrájimu kakor lev in kakor mlad lev Judovi hiši. Jaz, celó jaz, bom raztrgal in odšel proč, jaz bom odnesel in nihče ga ne bo rešil.
Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
15 Šel bom in se vrnil na svoj kraj, dokler ne bodo priznali svojega prestopka in iskali mojega obraza. V svoji stiski me bodo zgodaj iskali.«
Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”

< Ozej 5 >