< 1 Mojzes 7 >
1 Gospod je rekel Noetu: »Pridi ti in vsa tvoja hiša v ladjo, kajti pred seboj sem te videl pravičnega v tem rodu.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 Od vsake čiste živali boš vzel k sebi po sedmero, samca in njegovo samico. Od živali, ki niso čiste, po dvoje, samca in njegovo samico.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 Tudi od perjadi neba po sedmero, samca in samico, da na obličju vse zemlje ohraniš seme živo.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 Kajti še sedem dni in povzročil bom, da na zemljo dežuje štirideset dni in štirideset noči; in vsako živo snov, ki sem jo naredil, bom uničil izpred obličja zemlje.«
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Noe je storil glede na vse, kar mu je Gospod zapovedal.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Noe je bil star šeststo let, ko je bila na zemlji poplava vodá.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Noe je zaradi poplavnih vodá vstopil v ladjo in njegovi sinovi in njegova žena in žene njegovih sinov z njim.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Od čistih živali in od živali, ki niso čiste in od perjadi in od vsake stvari, ki se plazi na zemlji,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 so po dve in dve vstopile k Noetu v ladjo, samec in samica, kakor je Bog zapovedal Noetu.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Po sedmih dneh pa se je pripetilo, da so bile na zemlji poplavne vode.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 V šeststotem letu Noetovega življenja, v drugem mesecu, sedemnajsti dan meseca, istega dne so izbruhnili vsi studenci velike globine in okna neba so bila odprta.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 In dež je bil na zemlji štirideset dni in štirideset noči.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 Prav isti dan so vstopili v ladjo Noe ter Sem in Ham in Jafet, Noetovi sinovi in Noetova žena in z njim tri žene njegovih sinov.
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 Oni in vsaka žival po njeni vrsti in vsa živina po njeni vrsti in vsaka plazeča stvar, ki se plazi na zemlji, po njeni vrsti in vsaka perjad po njeni vrsti, vsaka ptica od vsake sorte.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Vstopile so k Noetu v ladjo, [po] dve in dve od vsega mesa, v katerem je dih življenja.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Te, ki so vstopile, so vstopile samec in samica od vsega mesa, kakor mu je Bog zapovedal. Gospod pa ga je zaprl noter.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Na zemlji je bila poplava štirideset dni. Vode so narasle in podpirale ladjo in ta je bila dvignjena nad zemljo.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Vode so prevladale in silno narasle na zemlji in ladja je plula na obličju vodá.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Vode so silno prevladale na zemlji in vsi visoki hribi, ki so bili pod celotnim nebom, so bili pokriti.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 Vode so se dvignile [in] prevladale [za] petnajst komolcev in gore so bile pokrite.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Umrlo je vse meso, ki se je gibalo na zemlji, tako od perjadi, od živine, od živali in od vsake plazeče stvari, ki se plazi na zemlji in vsakega človeka.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Vse, v čigar nosnicah je bil dih življenja, od vsega, kar [jih] je bilo na kopni zemlji, je umrlo.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 Uničena je bila vsaka živa snov, ki je bila na obličju tal, tako človek kakor živina, plazeče stvari in perjad neba; in bile so uničene z zemlje. Živ je ostal samo Noe in tisti, ki so bili z njim na ladji.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 Vode so prevladovale na zemlji sto petdeset dni.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.