< 1 Mojzes 4 >

1 Adam je spoznal svojo ženo Evo in ta je spočela ter rodila Kajna in rekla: »Dobila sem človeka od Gospoda.«
Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
2 In ponovno je rodila njegovega brata Abela. In Abel je bil čuvaj ovc, toda Kajn je bil orač tal.
Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
3 Tekom časa se je pripetilo, da je Kajn od sadu tal prinesel daritev Gospodu.
Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
4 In tudi Abel je prinesel prvence od svojega tropa in od njihove tolšče. In Gospod je imel spoštovanje do Abela in njegove daritve,
Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
5 toda do Kajna in njegove daritve [pa] ni imel spoštovanja. In Kajn je bil zelo ogorčen in njegovo obličje je upadlo.
amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
6 Gospod je rekel Kajnu: »Zakaj si ogorčen? In zakaj je tvoje obličje upadlo?
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
7 Če delaš dobro ali ne boš sprejet? Če pa ne delaš dobro, greh leži pri vratih. Njegovo poželenje naj bo k tebi, ti pa boš vladal nad njim.«
Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
8 Kajn je govoril s svojim bratom Abelom, in ko sta bila na polju, se je pripetilo, da se je Kajn dvignil zoper svojega brata Abela in ga ubil.
To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
9 Gospod je rekel Kajnu: »Kje je tvoj brat, Abel?« On pa je rekel: »Ne vem. Sem mar jaz čuvaj svojega brata?«
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
10 Rekel je: »Kaj si storil? Glas krvi tvojega brata iz tal vpije k meni.
Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
11 Sedaj si preklet pred zemljo, ki je odprla svoja usta, da iz tvoje roke sprejme kri tvojega brata.
Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
12 Ko boš oral tla, ti odslej ne bodo obrodila svoje moči; na zemlji boš ubežnik in potepuh.«
In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
13 Kajn je Gospodu rekel: »Moja kazen je večja, kakor jo lahko prenesem.
Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
14 Glej, danes si me napodil izpred obličja zemlje, in skrit bom pred tvojim obličjem, in na zemlji bom ubežnik ter potepuh; in zgodilo se bo, da me bo ubil vsak, kdor me najde.«
Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
15 Gospod mu je rekel: »Zatorej kdorkoli ubije Kajna, bo nanj nadeto sedemkratno maščevanje.« In Gospod je na Kajna namestil znamenje, da kdorkoli ga najde, ga ne bi ubil.
Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
16 Kajn je odšel izpred Gospodove prisotnosti in prebival v deželi Nod, vzhodno od Edena.
Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
17 Kajn je spoznal svojo ženo in ta je spočela ter rodila Henoha. Ta je zgradil mesto in ime mesta imenoval Henoh, po imenu svojega sina.
Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
18 Henohu se je rodil Irád, in Irád je zaplodil Mehujaéla, in Mehujaél je zaplodil Metušaéla, in Metušaél je zaplodil Lameha.
Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
19 Lameh si je vzel dve ženi: ime prve je bilo Ada, ime druge pa Cila.
Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
20 Ada je rodila Jabála; ta je bil oče teh, ki prebivajo v šotorih in teh, ki imajo živino.
Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
21 Ime njegovega brata je bilo Jubál; bil je oče vseh teh, ki prijemajo harfo in piščal.
Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
22 Cila pa je rodila tudi Tubál Kajina, učitelja vsakega rokodelca z bronom in železom, in Tubál Kajinova sestra je bila Naáma.
Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
23 Lameh je rekel svojima ženama, Adi in Cili: »Poslušajta moj glas, vidve, Lamehovi ženi, prisluhnita mojemu govoru, kajti umoril sem človeka, ki mi prizadeva rane in mladeniča, za mojo rano.
Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
24 Če bo Kajn sedemkrat maščevan, resnično, Lameh [pa] sedeminsedemdesetkrat.«
Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
25 Adam je spet spoznal svojo ženo in rodila je sina in njegovo ime je imenovala Set. »Kajti Bog, « je rekla, »mi je določil drugega potomca namesto Abela, ki ga je ubil Kajn.«
Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
26 In Setu, tudi njemu se je rodil sin, in njegovo ime je imenoval Enóš. Potem so ljudje začeli klicati Gospodovo ime.
Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.

< 1 Mojzes 4 >