< 1 Mojzes 19 >

1 Zvečer sta k Sódomi prišla dva angela in Lot je sedel pri sódomskih velikih vratih, in ko ju je Lot zagledal, je vstal, da ju sreča in se je s svojim obrazom upognil k tlom
Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
2 ter rekel: »Glejta torej, moja gospoda, vstopita, prosim vaju, v hišo svojega služabnika in ostanita vso noč in umijta svoja stopala in bosta zgodaj vstala ter nadaljevala po svojih poteh.« Onadva pa sta rekla: »Ne, temveč bova vso noč ostala na ulici.«
Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
3 Zelo ju je silil in obrnila sta se k njemu in vstopila v njegovo hišo in naredil jima je gostijo, spekel nekvašeni kruh in so jedli.
Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
4 Toda preden so se ulegli, so možje mesta, torej sódomski možje, obdali hišo, tako mladi kakor stari, vse ljudstvo iz vsake četrti.
Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
5 Klicali so k Lotu ter mu rekli: »Kje sta moža, ki sta to noč prišla k tebi? Privedi ju ven k nam, da ju bomo lahko spoznali.«
Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
6 Lot je od vrat odšel k njim in vrata zaprl za seboj
Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
7 ter rekel: »Prosim vas, bratje, ne storite tako zlobno.
ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
8 Glejte torej, imam dve hčeri, ki nista spoznali moža. Naj vam, prosim vas, njiju pripeljem k vam in storite jima, kakor je dobro v vaših očeh. Samo tema možema ne storite ničesar, kajti zato sta prišla pod senco moje strehe.«
Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
9 Rekli so: »Umakni se.« In ponovno so rekli: »Ta pajdaš je prišel, da začasno prebiva in hoče biti sodnik. Torej bomo s teboj postopali slabše kakor z njima.« In zelo so pritiskali na človeka, torej Lota in se približali, da zlomijo vrata.
Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
10 Toda moža sta iztegnila svojo roko in potegnila Lota k njim v hišo ter zaprla vrata.
Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
11 Može, ki so bili pri hišnih vratih, pa sta udarila s slepoto, tako male kakor velike, tako da so se utrudili, da bi našli vrata.
Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
12 Moža sta Lotu rekla: »Imaš, razen teh tukaj, še koga? Zeta, svoje sinove, svoje hčere in karkoli imaš v mestu, jih odvedi iz tega kraja,
Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
13 kajti uničila bova ta kraj, ker je njihovo vpitje naraslo pred Gospodovim obličjem in Gospod naju je poslal, da ga uničiva.«
gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
14 Lot je odšel ven in svojima zetoma, ki sta poročila njegovi hčeri, spregovoril ter rekel: »Vstanita, pojdita ven iz tega kraja, kajti Gospod bo to mesto uničil.« Toda videti je bil kakor nekdo, ki je zasmehoval svoja zeta.
Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
15 Ko je vstalo jutro, sta angela podvizala Lota, rekoč: »Vstani, vzemi svojo ženo in svoji dve hčeri, ki sta tukaj, da ne bi bil použit v krivičnosti tega mesta.«
Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
16 Medtem ko se je obotavljal, sta moža prijela njegovo roko, roko njegove žene in roki njegovih dveh hčera – Gospod mu je bil usmiljen – in odvedla sta ga naprej in ga postavila zunaj mesta.
Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
17 In pripetilo se je, ko sta jih privedla daleč naprej, da je rekel: »Pobegnite zaradi svojega življenja. Ne glejte za seboj niti ne ostanite na vsej ravnini. Zbežite h gori, da ne bi bili použiti.«
Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
18 Lot pa jima je rekel: »Oh ne tako, moj Gospod.
Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
19 Glej torej, tvoj služabnik je našel milost v tvojem pogledu in ti si poveličal svoje usmiljenje, ki si mi ga izkazal z rešitvijo mojega življenja, jaz pa ne morem pobegniti h gori, da me ne bi zajelo neko zlo in umrem.
Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
20 Glej torej, to mesto je blizu, da pobegnem vanj in to je majhno. Oh, dovoli mi pobegniti tja ( mar ni to majhno?) in moja duša bo živela.«
Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
21 Rekel mu je: »Glej, sprejel sem te tudi glede te stvari, da ne bom uničil tega mesta, za katero si govoril.
Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
22 Pohiti, zbeži tja, kajti ničesar ne morem storiti, dokler ne prideš tja.« Zato je bilo ime tega mesta imenovano Coar.
Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
23 Sonce je vstalo nad zemljo, ko je Lot vstopil v Coar.
A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
24 Potem je Gospod na Sódomo in na Gomóro deževal žveplo in ogenj od Gospoda z neba
Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
25 in razdejal je ti mesti, vso ravnino, vse prebivalce mest in to, kar je raslo na tleh.
Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
26 Toda njegova žena je za njim pogledala nazaj in postala solnat steber.
Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
27 Abraham je vstal zgodaj zjutraj h kraju, kjer je stal pred Gospodom
Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
28 in pogledal proti Sódomi in Gomóri in proti vsej deželi ravnine in zagledal in glej, dim dežele se je dvigal kakor dim iz talilne peči.
Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
29 In pripetilo se je, ko je Bog uničil mesta ravnine, da se je Bog spomnil Abrahama in Lota poslal iz srede razdejanja, ko je razdejal mesti, v katerih je prebival Lot.
Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
30 Lot je iz Coarja odšel navzgor, prebival na gori in njegovi hčeri z njim, kajti bal se je prebivati v Coarju in prebival je v votlini, on in njegovi dve hčeri.
Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
31 Prvorojena je rekla mlajši: »Najin oče je star in tukaj ni moškega na zemlji, da pride noter v naju po navadi vse zemlje.
Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
32 Pridi, najinega očeta pripraviva piti vino in bova ležali z njim, da lahko ohraniva seme najinega očeta.«
Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
33 To noč sta svojega očeta pripravili piti vino in vstopila je prvorojena in ležala s svojim očetom in ni zaznal, ne ko se je ulegla, ne ko je vstala.
A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
34 Naslednji dan se je pripetilo, da je prvorojena rekla mlajši: »Glej, sinoči sem bila s svojim očetom. Pripraviva ga tudi to noč piti vino in pojdi ti in lezi z njim, da bova lahko ohranili seme najinega očeta.«
Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
35 Tudi to noč sta svojega očeta pripravili piti vino in mlajša je vstala in ležala z njim in ni zaznal, ne ko se je ulegla, ne ko je vstala.
Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
36 Tako sta bili obe Lotovi hčeri z otrokom s svojim očetom.
Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
37 Prvorojena je rodila sina in njegovo ime imenovala Moáb. Isti je oče Moábcev do današnjega dne.
’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
38 Mlajša, tudi ona je rodila sina in njegovo ime imenovala Ben Amí. Isti je oče Amónovih otrok do današnjega dne.
’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.

< 1 Mojzes 19 >