< Ezekiel 37 >
1 Gospodova roka je bila nad menoj in me odvedla ven v Gospodovem duhu in me postavila dol v sredo doline, ki je bila polna kosti
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 in dal mi je, da sem šel okoli njih. In glej, tam jih je bilo zelo veliko v odprti dolini. In glej, bile so zelo suhe.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 Rekel mi je: »Človeški sin, ali lahko te kosti živijo?« Odgovoril sem: »Oh Gospod Bog, ti veš.«
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Ponovno mi je rekel: »Prerokuj nad temi kostmi in jim reci: ›Oh ve, suhe kosti, poslušajte Gospodovo besedo.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Tako govori Gospod Bog tem kostem: ›Glejte, povzročil bom, da v vas vstopi dih in boste živele.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 Na vas bom položil kite in privedel meso na vas in vas pokril s kožo in položil dih v vas in ve boste živele in spoznale boste, da jaz sem Gospod.‹«
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 Tako sem prerokoval, kakor mi je bilo zapovedano. Ko sem prerokoval, je bil tam hrup in glej tresenje in kosti so prišle skupaj, kost k svoji kosti.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 In ko sem gledal, glej, kite in meso so prišli nanje in zgoraj jih je pokrila koža, toda v njih ni bilo diha.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Potem mi je rekel: »Prerokuj vetru, prerokuj, človeški sin in reci vetru: ›Tako govori Gospod Bog: ›Pridi iz štirih vetrov, oh dih in dihni na te umorjene, da bodo lahko živeli.‹«
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 Tako sem prerokoval, kakor mi je zapovedal in dih je prišel vanje in oživeli so in vstali na svoja stopala, silno velika vojska.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Potem mi je rekel: »Človeški sin, te kosti so celotna Izraelova hiša. Glej, govorijo: ›Naše kosti so suhe in naše upanje je izgubljeno. Odrezani smo iz svoje dežele.‹
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Zato prerokuj in jim reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Glej, oh moje ljudstvo, odprl bom vaše grobove in povzročim vam, da pridete iz svojih grobov in vas privedem v Izraelovo deželo.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 In vi boste spoznali, da jaz sem Gospod, ko odprem vaše grobove, oh moje ljudstvo in vas privedel gor, ven iz vaših grobov.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 Svojega duha bom položil v vas in boste živeli in namestil vas bom v vašo lastno deželo. Potem boste vedeli, da sem jaz, Gospod, to govoril in to izvêdel, govori Gospod.‹«
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 Beseda Gospodova je ponovno prišla k meni, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 »Poleg tega si ti, človeški sin, vzemi eno palico in nanjo napiši: ›Za Juda in za Izraelove otroke, njegove družabnike.‹ Potem vzemi drugo palico in nanjo napiši: ›Za Jožefa, Efrájimovo palico in za vso Izraelovo hišo njegovih družabnikov.‹
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 Pridruži ju eno k drugi, v eno palico; in postali bosta eno v tvoji roki.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 In ko ti bodo otroci tvojega ljudstva govorili, rekoč: ›Ali nam ne boš pokazal, kaj misliš s tem?‹
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 jim reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Glejte, vzel bom Jožefovo palico, ki je v Efrájimovi roki in Izraelove rodove, njegove rojake in jih položil z njim, celó z Judovo palico in jih naredil eno palico in oni bodo eno v moji roki.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 In palici, na kateri pišeš, bosta v tvoji roki pred njihovimi očmi.‹
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 In reci jim: ›Tako govori Gospod Bog: ›Glej vzel bom Izraelove otroke izmed poganov, kamor so odšli in zbral jih bom na vsaki strani in jih privedel v njihovo lastno deželo.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 In naredil jih bom en narod v deželi, na Izraelovih gorah; in en kralj bo kralj nad njimi vsemi, in ne bodo več dva naroda niti sploh ne bodo več razdeljeni v dve kraljestvi.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Niti se ne bodo več omadeževali s svojimi maliki niti s svojimi ostudnimi stvarmi niti s katerimikoli izmed njihovih prestopkov, temveč jih bom rešil iz vseh njihovih bivališč, v katerih so grešili in jih bom očistil. Tako bodo moje ljudstvo in jaz bom njihov Bog.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 Moj služabnik David bo kralj nad njimi; in vsi bodo imeli enega pastirja. Prav tako se bodo ravnali po mojih sodbah in obeleževali moje zakone in jih izvajali.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 In prebivali bodo v deželi, ki sem jo dal Jakobu, svojemu služabniku, v kateri so prebivali vaši očetje; in prebivali bodo tam, celó oni, njihovi otroci in otroci njihovih otrok na veke, in moj služabnik David bo njihov princ na veke.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 Poleg tega bom z njimi sklenil zavezo miru. To bo večna zaveza z njimi in jaz jih bom namestil in jih pomnožil in svoje svetišče bom postavil v njihovi sredi na vékomaj.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 Prav tako bo z njimi moje šotorsko svetišče. Da, jaz bom njihov Bog in oni bodo moje ljudstvo.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 In pogani bodo spoznali, da jaz, Gospod, posvečujem Izraela, ko bo moje svetišče v njihovi sredi na vékomaj.‹«
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”