< Ezekiel 29 >

1 V desetem letu, v desetem mesecu, na dvanajsti dan meseca je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 »Človeški sin, naravnaj svoj obraz proti faraonu, egiptovskemu kralju in prerokuj zoper njega in zoper ves Egipt.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Govori in reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Glej, jaz sem zoper tebe, faraon, egiptovski kralj, veliki zmaj, ki ležiš v sredi svojih rek, ki praviš: ›Moja reka je moja lastna in naredil sem jo zase.‹
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Toda dal ti bom kavlje v čeljusti in ribam tvojih rek bom povzročil, da se prilepijo na tvoje luskine in izvlekel te bom iz srede tvojih rek in vse ribe tvojih rek se bodo prilepile na tvoje luskine.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 In pustil te bom vreči v divjino, tebe in vse ribe tvojih rek. Padel boš na odprta polja; ne boš zbližan niti ne zbran. Dal sem te za hrano poljskim živalim in perjadi neba.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 In vsi prebivalci Egipta bodo spoznali, da jaz sem Gospod, ker so bili trstična palica za Izraelovo hišo.‹
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 Kadar so te prijeli za tvojo roko, si se zlomil in raztrgal vso njihovo ramo, in ko so se oprli nate, si se zlomil in storil, da vsa njihova ledja odrevenijo.‹
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Zato tako govori Gospod Bog: ›Glej, nadte bom privedel meč in iz tebe iztrebil človeka in žival.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 In egiptovska dežela bo zapuščena in opustošena; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod, ker je rekel: ›Reka je moja in jaz sem jo naredil.‹
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Glej, zato sem zoper tebe in zoper tvoje reke in egiptovsko deželo bom naredil popolnoma opustošeno in zapuščeno od Siénskega stolpa celó do meje Etiopije.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Skoznjo ne bo šlo nobeno človeško stopalo niti ne bo šlo skozi živalsko stopalo niti štirideset let ne bo naseljena.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 In egiptovsko deželo bom naredil zapuščeno v sredi pokrajin, ki so zapuščene in njena mesta, med mesti, ki so opustošena, bodo zapuščena štirideset let in Egipčane bom razkropil med narode in jih razpodil po pokrajinah.‹
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 Vendar tako govori Gospod Bog: ›Ob koncu štiridesetih let bom zbral Egipčane izmed ljudstev, kamor so bili razkropljeni,
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 in ponovno bom privedel ujetništvo Egipta in povzročil jim bom, da se vrnejo v deželo Patrós, v deželo svojega prebivališča; in tam bodo nizko kraljestvo.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 To bo najnižje izmed kraljestev niti se ne bo več povzdigovalo nad narodi, kajti jaz jih bom zmanjšal, da ne bodo več vladali nad narodi.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 In le-to ne bo več zaupanje Izraelove hiše, ki v spomin prinaša njihovo krivičnost, ko bodo gledali za njimi, toda spoznali bodo, da jaz sem Gospod Bog.‹«
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 Pripetilo se je v sedemindvajsetem letu, v prvem mesecu, na prvi dan meseca, [da] je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 »Človeški sin, babilonski kralj Nebukadnezar je svoji vojski storil, da služi sijajno službo zoper Tir. Vsaka glava je bila narejena plešasto in vsaka rama je bila oluščena, vendar ni imel nobenih plačil niti njegova vojska za Tir, za službo, ki jo je opravil zoper njega.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Zato tako govori Gospod Bog: ›Glej, egiptovsko deželo bom dal Nebukadnezarju, babilonskemu kralju; in on bo zajel njeno množico in vzel njeno ukradeno blago in vzel njen plen; in to bodo plačila za njegovo vojsko.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Izročil sem mu egiptovsko deželo za njegov trud, s katerim je služil zoper njo, ker so delali zame, ‹ govori Gospod Bog.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 ›Na tisti dan bom rogu Izraelove hiše povzročil, da vzbrsti in jaz ti bom dal odprtje ust v njihovi sredi, in spoznali bodo, da jaz sem Gospod.‹«
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 29 >