< Ezekiel 16 >
1 Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 »Človeški sin, povzroči [prestolnici] Jeruzalem, da spozna svoje ogabnosti
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 in reci: ›Tako govori Gospod Bog [prestolnici] Jeruzalem: ›Tvoj rod in tvoje rojstvo je iz kánaanske dežele; tvoj oče je bil Amoréjec, tvoja mati pa Hetejka.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Glede tvojega rojstva, na dan, ko si bila rojena, tvoj popek ni bil odrezan niti nisi bila umita v vodi, da ti omehča [kožo]; sploh nisi bila odrgnjena s soljo niti povita.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Niti se te nobeno oko ni usmililo, da bi ti storilo karkoli od tega, da bi imelo do tebe sočutje; temveč si bila vržena na odprto polje, do gnusenja glede tvoje osebe, na dan, ko si bila rojena.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 In ko sem šel mimo tebe in te videl oskrunjeno v svoji krvi, sem ti rekel, ko si bila v svoji krvi: ›Živi; ‹ da, rekel sem ti, ko si bila v svoji krvi: ›Živi.‹
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Dal sem ti, da si se namnožila kakor brstje polja in povečala si se in postala velika in prišla k odličnim ornamentom. Tvoje prsi so se oblikovale in tvoji lasje so zrasli, medtem ko si bila naga in gola.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Torej, ko sem šel mimo tebe in pogledal nate, glej, tvoj čas je bil čas ljubezni. Razširil sem krajec svojega oblačila nad teboj in pokril tvojo nagoto. Da, prisegel sem ti in vstopil v zavezo s teboj, ‹ govori Gospod Bog ›in postala si moja.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Potem sem te umil z vodo; da, temeljito sem izmil tvojo kri iz tebe in te mazilil z oljem.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Oblekel sem te tudi z izvezenim delom in ti obul jazbečevo kožo in te naokoli opasal s tankim lanenim platnom in te ogrnil s svilo.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Odel sem te tudi z ornamenti in na tvoje roke sem nataknil zapestnice in verižico na tvoj vrat.
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 Položil sem dragulj na tvoje čelo in uhane v tvoja ušesa in krasno krono na tvojo glavo.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Tako si bila odeta z zlatom in srebrom, in tvoje oblačilo je bilo iz tankega lanenega platna, svile in izvezenega dela. Jedla si fino moko, med in olje. Bila si silno krasna in uspevala si v kraljestvu.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Tvoj ugled je zaradi tvoje lepote odšel naprej med pogane, kajti ta je bila popolna zaradi moje ljubkosti, ki sem jo položil nadte, ‹ govori Gospod Bog.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 ›Toda zaupala si v svojo lastno lepoto in igrala pocestnico zaradi svojega ugleda in svoje prešuštvovanje si izlila na vsakega, ki je šel mimo; njegovo je bilo.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Vzela si od svojih oblek in svoje visoke kraje si odela s številnimi barvami in na njih igrala pocestnico. Podobne stvari ne bodo prišle niti to ne bo tako.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Vzela si tudi svoje lepe dragocenosti od mojega zlata in od mojega srebra, ki sem ti jih dal in si si naredila moške podobe in z njimi zagrešila vlačugarstvo
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 in jemala si svoje izvezene obleke in jih pokrivala in prednje si postavljala moje olje in moje kadilo.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Tudi moja hrana, ki sem ti jo dal, fina moka, olje in med, s katero sem te hranil, celo to si postavljala prednje v prijeten vonj. In tako je to bilo, ‹ govori Gospod Bog.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 ›Poleg tega si jemala svoje sinove in svoje hčere, ki si mi jih rodila in te si jim žrtvovala, da bi bili požrti. Je to izmed tvojih vlačugarstev majhna zadeva,
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 da si morila moje otroke in jim jih izročala, da gredo zanje skozi ogenj?
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 In v vseh svojih ogabnostih in svojih vlačugarstvih se nisi spomnila dni svoje mladosti, ko si bila naga in gola in si bila oskrunjena v svoji krvi.‹
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 In pripetilo se je po vseh tvojih zlobnostih (gorje, gorje tebi!‹ govori Gospod Bog ),
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 da si si zgradila tudi eminenten kraj in si si naredila visok kraj na vsaki ulici.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 Visok kraj si si zgradila na vsakem začetku poti in storila si, da je bila tvoja lepota prezirana in svoja stopala si razprla vsakemu, ki je šel mimo in pomnožila si svoja vlačugarstva.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Prav tako si zagrešila prešuštvovanje z Egipčani, svojimi sosedi velikega uda in svoja vlačugarstva si povečala, da bi me dražila do jeze.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Glej, zato sem nad teboj iztegnil svojo roko in zmanjšal tvojo vsakdanjo hrano in te izročil volji tistih, ki te sovražijo, hčeram Filistejcev, ki se sramujejo tvojih nespodobnih poti.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Vlačugo si igrala tudi z Asirci, ker si bila nenasitna; da, z njimi si igrala pocestnico, pa vendar nisi mogla biti potešena.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Poleg tega si pomnožila svoje prešuštvovanje v kánaanski deželi do Kaldeje; in vendar nisi bila potešena s tem.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Kako šibko je tvoje srce, ‹ govori Gospod Bog, ›glede na to, da počneš vse te stvari, delo gospodovalne vlačugarske ženske;
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 v tem, da si gradiš svoje eminentne kraje na začetku vsake poti in si delaš svoje visoke kraje na vsaki ulici; in nisi bila kot pocestnica, v tem, da preziraš plačilo,
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 temveč kakor žena, ki zagreši zakonolomstvo, ki jemlje tujce namesto svojega soproga!
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 Oni dajejo darila vsem vlačugam, toda ti daješ svoja darila vsem svojim ljubimcem in jih najemaš, da lahko pridejo k tebi na vsaki strani zaradi tvojega vlačugarstva.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 In v tvojem vlačugarstvu je v tebi nasprotje od drugih žensk, da zagrešiš vlačugarstva, medtem ko ti nihče ne sledi, in pri tem ti daješ nagrado, tebi pa ni dana nobena nagrada, zato si nasprotje.‹
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 Zatorej, oh pocestnica, poslušaj besedo od Gospoda:
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 ›Tako govori Gospod Bog: ›Ker je bila tvoja umazanost izlita in tvoja nagota odkrita zaradi tvojega vlačugarstva s tvojimi ljubimci in z vsemi maliki tvojih ogabnosti in s krvjo tvojih otrok, ki si jim jih dala;
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 glej, zato bom zbral vse tvoje ljubimce, s katerimi si uživala in vse tiste, ki si jih ljubila, z vsemi tistimi, ki si jih sovražila; jaz jih bom celo zbral naokoli tebe zoper tebe in jim odkril tvojo nagoto, da bodo lahko videli vso tvojo nagoto.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Sodil te bom, kakor so sojene ženske, ki prelomijo zakonsko zvezo in prelijejo kri; in dal ti bom kri v razjarjenosti in ljubosumnosti.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Prav tako te bom izročil v njihovo roko in zrušili bodo tvoj eminenten kraj in zlomili tvoje visoke kraje. Slekli te bodo tudi iz tvojih oblačil in vzeli tvoje lepe dragocenosti in te pustili nago in golo.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Prav tako bodo zoper tebe privedli skupino in te bodo kamnali s kamni in te prebodli s svojimi meči.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Tvoje hiše bodo požgali z ognjem in izvršili sodbe nad teboj v očeh mnogih žensk. Povzročil ti bom, da prenehaš z igranjem pocestnice in tudi nobenega plačila ne boš več dajala.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Tako bom svoji razjarjenosti zoper tebe naredil, da počiva in moja ljubosumnost bo odšla od tebe in bom miren in ne bom več jezen.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Ker se nisi spomnila dni svoje mladosti, temveč si me razburjala v vseh teh stvareh; glej, zato bom tudi jaz poplačal tvojo pot na tvoji glavi, ‹ govori Gospod Bog: ›in ne boš zagrešila te nespodobnosti nad vsemi svojimi ogabnostmi.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Glej, vsak, kdor uporablja pregovore, bo ta pregovor uporabil zoper tebe, govoreč: ›Kakršna je mati, takšna je njena hči.‹
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Ti si hči svoje matere, ki prezira svojega soproga in svoje otroke; in ti si sestra svojih sestrá, ki so prezirale svoje soproge in svoje otroke. Tvoja mati je bila Hetejka in tvoj oče Amoréjec.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Tvoja starejša sestra je Samarija, ona in njene hčere, ki prebivajo na tvoji levici. Tvoja mlajša sestra, ki prebiva pri tvoji desnici, je Sódoma in njene hčere.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Vendar nisi hodila po njihovih poteh niti storila po njihovih ogabnostih. Temveč kot bi bila to malenkost, si bila bolj izprijena kakor one na vseh svojih poteh.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Kakor jaz živim, ‹ govori Gospod Bog, ›niti tvoja sestra Sódoma niti njene hčere niso počele, kakor si storila ti in tvoje hčere.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Glej, to je bila krivičnost tvoje sestre Sódome, ponos, polnost kruha, obilje brezdelja v njej in v njenih hčerah niti ni krepila roke ubogega in pomoči potrebnega.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Bile so ošabne in zagrešile ogabnost pred menoj, zato sem jih vzel proč, kakor se mi je videlo dobro.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Niti ni Samarija zagrešila polovice tvojih grehov, temveč si pomnožila svoje ogabnosti bolj kakor oni [dve] in opravičila si svoji sestri v vseh svojih ogabnostih, ki si jih storila.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Tudi ti, ki si sodila svoji sestri, nosi svojo lastno sramoto za svoje grehe, ki si jih zagrešila bolj gnusno kakor oni [dve]. Oni sta pravičnejši kakor ti. Da, tudi ti bodi zbegana in nosi svojo sramoto v tem, da si opravičila svoji sestri.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Ko bom ponovno privedel njihovo ujetništvo, ujetništvo Sódome in njenih hčera in ujetništvo Samarije in njenih hčera, takrat bom ponovno privedel ujetništvo tvojih ujetnikov v njihovi sredi,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 da boš lahko nosila svojo lastno sramoto in boš lahko zbegana v vsem, kar si storila, v tem, da si jima tolažba.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Ko se bodo tvoje sestre, Sódoma in njene hčere, vrnile k svojemu prejšnjemu stanju in se bodo Samarija in njene hčere vrnile k svojemu prejšnjemu stanju, takrat se boste ti in tvoje hčere vrnile k svojemu prejšnjemu stanju.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Kajti tvoja sestra Sódoma ni bila omenjena s tvojimi usti na dan tvojega ponosa,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 preden je bila odkrita tvoja zlobnost, kakor ob času, ko so te grajale sirske hčere in vsi tisti, ki so okrog nje, hčere Filistejcev, ki te prezirajo vsenaokrog.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Nosila si svojo nespodobnost in svoje ogabnosti, ‹ govori Gospod.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Kajti tako govori Gospod Bog: ›S teboj bom postopal celo kakor si ti storila, ki si prezirala prisego v prelamljanju zaveze.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Kljub temu se bom spomnil svoje zaveze s teboj v dneh tvoje mladosti in osnoval ti bom večno zavezo.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Potem se boš spomnila svojih poti in boš osramočena, ko boš sprejela svoje sestre, svoje starejše in svoje mlajše, in dal ti jih bom za hčere, toda ne s tvojo zavezo.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 S teboj bom utrdil svojo zavezo in vedela boš, da jaz sem Gospod,
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 da se lahko spomniš in boš zbegana in zaradi svoje sramote nikoli več ne boš odprla svojih ust, ko bom pomirjen proti tebi za vse, kar si storila, ‹ govori Gospod Bog.‹«
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”