< Ezekiel 12 >
1 Prav tako je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
2 »Človeški sin, prebivaš v sredi uporne hiše, ki imajo oči, da vidijo, pa ne vidijo; imajo ušesa, da slišijo, pa ne slišijo, kajti uporna hiša so.
ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
3 Zato, človeški sin, si pripravi stvari za selitev in se preseli podnevi, v njihovem pogledu; in preselil se boš iz svojega kraja na drug kraj, v njihovem pogledu. Morda bodo to preudarili, kajti uporna hiša so.
“Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
4 Potem boš podnevi prinesel svoje stvari, v njihovem pogledu, kakor stvari za selitev, in zvečer boš šel naprej, v njihovem pogledu, kakor tisti, ki gredo naprej v ujetništvo.
Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
5 Prekoplji se skozi steno, v njihovem pogledu in tam odnesi ven.
Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
6 V njihovem pogledu boš to nosil na svojih ramenih in to boš prenašal naprej v mraku. Pokril si boš svoj obraz, da ne vidiš tal, kajti postavil sem te za znamenje Izraelovi hiši.«
Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
7 In storil sem tako, kakor mi je bilo zapovedano. Podnevi sem prinesel svoje stvari, kakor stvari za v ujetništvo, zvečer pa sem se s svojo roko prekopál skozi zid; to sem prinesel naprej v mraku in to sem nosil na svojem ramenu, v njihovem pogledu.
Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
8 In zjutraj mi je prišla beseda od Gospoda, rekoč:
Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 »Človeški sin, ali ti ni Izraelova hiša, uporna hiša, rekla: ›Kaj delaš?‹
“Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
10 Povej jim: ›Tako govori Gospod Bog: ›To breme zadeva princa v [prestolnici] Jeruzalem in vso Izraelovo hišo, ki so med njimi.‹
“Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
11 Reci: ›Jaz sem vaše znamenje. Kakor sem jaz storil, tako bo storjeno njim. Odselili se bodo in odšli v ujetništvo.
Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
12 In princ, ki je med njimi, bo v mraku nosil na svojem ramenu in bo šel naprej. Prekopali bodo skozi zid, da bi tamkaj nosili ven skozi steno. Pokril si bo svoj obraz, da s svojimi očmi ne bo videl tal.
“Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
13 Tudi svojo mrežo bom razširil nad njim in zajet bo v mojo zanko, in privedel ga bom v Babilon, v deželo Kaldejcev; vendar je ne bo videl, čeprav bo tam umrl.
Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
14 In vse, ki so okoli njega, da mu pomagajo, bom razkropil proti vsakemu vetru in vse njegove čete; in za njimi bom izvlekel meč.
Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
15 In spoznali bodo, da jaz sem Gospod, ko jih bom razkropil med narode in jih razpršil v dežele.
“Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
16 Toda izločil bom peščico ljudi izmed njih pred mečem, pred lakoto in kužno boleznijo; da bodo med pogani, kamor pridejo, lahko razglasili vse svoje ogabnosti; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod.‹«
Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
17 Poleg tega je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 »Človeški sin, svoj kruh jej z drgetanjem in svojo vodo pij s trepetanjem in previdnostjo;
“Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
19 in povej ljudstvu dežele: ›Tako govori Gospod Bog o prebivalcih [prestolnice] Jeruzalem in o Izraelovi deželi: ›Svoj kruh bodo jedli s previdnostjo in svojo vodo pili z osuplostjo, da bo njihova dežela lahko zapuščena od vseh, ki so v njej, zaradi nasilja vseh tistih, ki prebivajo v njej.
Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
20 In mesta, ki so naseljena, bodo opustošena in dežela bo zapuščena; in spoznali boste, da jaz sem Gospod.‹«
Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
21 In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
22 »Človeški sin, kakšen je ta pregovor, ki ga imate v Izraelovi deželi, rekoč: ›Dnevi so podaljšani in vsako videnje odpove?‹
“Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
23 Povej jim torej: ›Tako govori Gospod Bog: ›Temu pregovoru bom storil, da preneha in ne bodo ga več uporabljali kot pregovor v Izraelu; temveč jim reci: ›Blizu so dnevi in učinek vsakega videnja.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
24 Kajti nobenih praznih videnj ne bo več niti laskajočih vedeževanj znotraj Izraelove hiše.
Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
25 Kajti jaz sem Gospod. Jaz bom govoril in beseda, ki jo bom govoril, se bo izpolnila; ta se ne bo več odlagala, kajti v vaših dneh, oh uporna hiša, bom rekel besedo in jo izpolnil, govori Gospod Bog.‹«
Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
26 Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
27 »Človeški sin, glej, tisti iz Izraelove hiše pravijo: ›Videnje, ki ga on vidi, je za mnoge dni, ki pridejo in prerokuje o časih, ki so še daleč.‹
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
28 Zato jim reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Nobena izmed mojih besed se ne bo več odlagala, temveč se bo beseda, ki sem jo govoril, izpolnila, ‹ govori Gospod Bog.«
“Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”