< 5 Mojzes 5 >

1 Mojzes je sklical ves Izrael in jim rekel: »Poslušaj, oh Izrael, zakone in sodbe, ki jih ta dan govorim v vaša ušesa, da se jih lahko naučite in jih ohranjate in jih izvršujete.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 Gospod, naš Bog, je z nami sklenil zavezo na Horebu.
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 Gospod te zaveze ni sklenil z našimi očeti, temveč z nami, torej nami, ki smo, vsi izmed nas, ta dan tukaj živi.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 Gospod je s teboj govoril iz obličja v obličje, na gori, iz srede ognja
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 (ob tistem času sem stal med Gospodom in vami, da bi vam pokazal Gospodovo besedo, kajti vi ste se zaradi ognja bali in niste šli gor na goro), rekoč:
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 ›Jaz sem Gospod, tvoj Bog, ki te je privedel iz egiptovske dežele, iz hiše sužnosti.
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 Pred menoj ne boš imel nobenih drugih bogov.
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 Sebi ne boš naredil nobene rezane podobe ali kakršnekoli podobnosti katerekoli stvari, ki je v nebesih zgoraj ali ki je na zemlji spodaj ali ki je v vodah pod zemljo.
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 Ne boš se jim priklanjal niti jim služil, kajti jaz, Gospod, tvoj Bog, sem ljubosumen Bog, ki obiskujem krivičnost očetov na otrocih do tretjega in četrtega rodu teh, ki me sovražijo
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 in izkazujem usmiljenje tisočim tistih, ki me ljubijo in varujejo moje zapovedi.
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 Ne boš v prazno vzel imena Gospoda, svojega Boga, kajti Gospod ne bo brez krivde držal tistega, ki v prazno jemlje njegovo ime.
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Varuj šabatni dan, da ga posvečuješ, kakor ti je zapovedal Gospod, tvoj Bog.
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 Šest dni se boš trudil in opravljal vse svoje delo,
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 toda sedmi dan je šabat Gospodu, tvojemu Bogu. Na [ta dan] ne boš opravljal nobenega dela, ne ti, niti tvoj sin, niti tvoja hči, niti tvoj sluga, niti tvoja dekla, niti tvoj vol, niti tvoj osel, niti nobena izmed tvoje živine, niti tvoj tujec, ki je znotraj tvojih velikih vrat, da lahko tvoj sluga in tvoja dekla počivata kakor ti.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 Spominjaj pa se, da si bil služabnik v egiptovski deželi in da te je Gospod, tvoj Bog, od tam privedel z mogočno roko in z iztegnjenim laktom. Zato ti je Gospod, tvoj Bog, zapovedal, da izvajaš šabatni dan.
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Spoštuj svojega očeta in svojo mater, kakor ti je zapovedal Gospod, tvoj Bog, da bodo tvoji dnevi lahko podaljšani in da ti bo dobro šlo v deželi, ki ti jo daje Gospod, tvoj Bog.
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 Ne boš ubil.
Kada ka yi kisankai.
18 Niti ne boš zagrešil zakonolomstva.
Kada ka yi zina.
19 Niti ne boš kradel.
Kada ka yi sata.
20 Niti ne boš pričal po krivem zoper svojega bližnjega.
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 Niti si ne boš želel žene svojega bližnjega, niti ne boš hlepel [po] hiši svojega bližnjega, [po] njegovem polju ali [po] njegovem slugi ali [po] njegovi dekli, [po] njegovem volu ali [po] njegovem oslu ali [po] katerikoli stvari, ki je [od] tvojega bližnjega.‹
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 Te besede je Gospod govoril vsemu zboru na gori, iz srede ognja, iz oblaka in iz goste teme, z močnim glasom. In ni več dodal. Napisal jih je na dve kamniti plošči in mi ju izročil.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 Pripetilo se je, ko ste iz srede teme zaslišali glas (kajti gora je gorela z ognjem), da ste se mi približali, celó vsi poglavarji vaših rodov in vaše starešine
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 in ste rekli: ›Glej, Gospod, naš Bog, nam je pokazal svojo slavo in svojo veličino in iz srede ognja smo slišali njegov glas. Ta dan smo videli, da Bog govori z možem in ta živi.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 Zdaj torej zakaj naj bi umrli? Kajti ta velik ogenj nas bo použil. Če še naprej slišimo glas Gospoda, našega Boga, potem bomo umrli.
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 Kajti kdo je tam od vsega mesa, ki je iz srede ognja slišal govoriti glas živega Boga, kakor smo mi in je živel?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Ti pojdi blizu in prisluhni vsemu, kar bo rekel Gospod, naš Bog in spregovori nam vse, kar ti bo govoril Gospod, naš Bog in mi bomo temu prisluhnili in to storili.‹
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 Gospod je slišal glas vaših besed, ko ste mi govorili in Gospod mi je rekel: ›Slišal sem glas besed tega ljudstva, ki so ti jih govorili. Dobro so povedali vse, kar so govorili.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 Oh, da bi bilo takšno srce v njih, da bi se me bali in se vedno držali vseh mojih zapovedi, da bi bilo lahko dobro z njimi in z njihovimi otroki na veke!
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Pojdi, reci jim: ›Ponovno se vrnite v svoje šotore.‹
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 Toda kar se tebe tiče, ti ostani tukaj, poleg mene in govoril ti bom vse zapovedi, zakone in sodbe, ki jih boš učil, da jih bodo lahko izpolnjevali v deželi, ki sem jim jo dal, da jo vzamejo v last.‹
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 Obeleževali boste torej, da delate, kakor vam je zapovedal Gospod, vaš Bog. Ne boste se odvrnili vstran, ne k desni roki ne k levi.
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 Hodili boste po vseh poteh, ki vam jih je zapovedal Gospod, vaš Bog, da boste lahko živeli in da bo lahko dobro z vami in da boste lahko podaljšali svoje dni v deželi, ki jo boste vzeli v last.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.

< 5 Mojzes 5 >