< 5 Mojzes 17 >
1 Gospodu, svojemu Bogu, ne boš žrtvoval nobenega bika ali ovce, na kateri je pomanjkljivost ali kakršnakoli slaba stvar, kajti to je ogabnost Gospodu, tvojemu Bogu.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 Če se med vami najdeta mož ali ženska, znotraj katerihkoli izmed tvojih velikih vrat, ki ti jih daje Gospod, tvoj Bog, ki sta storila zlobnost v očeh Gospoda, tvojega Boga, v tem, da sta prestopala njegovo zavezo
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 in sta šla in služila drugim bogovom in jih oboževala ali sonce ali luno ali katerokoli vojsko neba, česar nisem zapovedal
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 in ti je to povedano in si o tem slišal in marljivo poizvedoval in glej, če je resnično in je stvar gotova, da je v Izraelu narejena takšna ogabnost,
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 potem boš tega moža ali to žensko, ki sta zagrešila to zlobno stvar, pripeljal naprej, k svojim velikim vratom, torej tistega moža ali tisto žensko in ju boš kamnal s kamni, dokler ne umreta.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 Po ustih dveh ali treh prič bo tisti, ki je vreden smrti, usmrčen, toda po ustih ene priče ne bo usmrčen.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 Roke prič bodo prve nad njim, da ga usmrtijo in potem roke vsega ljudstva. Tako boš odstranil zlo izmed vas.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 Če tam vstane zadeva, v sodbi zate pretežka, med krvjo in krvjo, med izgovorom in izgovorom, med udarcem in udarcem, ki so zadeve polemike znotraj tvojih velikih vrat, potem se boš vzdignil in se povzpel na kraj, ki ga bo Gospod, tvoj Bog, izbral
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 in prišel boš k duhovnikom Lévijevcem in k sodniku, ki bo v tistih dneh in povprašal in pokazali ti bodo razsodbo sodbe.
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 Storil boš glede na razsodbo, ki ti jo bodo pokazali tisti, iz tistega kraja, ki ga bo Gospod izbral in obeleževal boš, da storiš glede na vse, o čemer te obvestijo.
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 Storil boš glede na razsodbo postave, ki te jo bodo učili, in glede na sodbo, ki ti jo bodo povedali. Ne boš se odvrnil od obsodbe, ki ti jo bodo pokazali, ne na desno roko niti ne na levo.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 Mož pa, ki bo delal prepotentno in ne bo prisluhnil duhovniku, ki tam stoji, da služi pred Gospodom, tvojim Bogom ali sodniku, celo tisti mož bo umrl, in ti se boš iz Izraela znebil zla.
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 In vse ljudstvo bo slišalo in se balo in ne bo več prepotentno ravnalo.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 Ko prideš v deželo, ki ti jo daje Gospod, tvoj Bog in jo boš vzel v last in boš prebival v njej in boš rekel: ›Nad seboj si bom postavil kralja, kakor je pri vseh narodih naokoli mene, ‹
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 boš vsekakor za kralja nad seboj postavil tistega, ki ga bo izbral Gospod, tvoj Bog. Enega izmed svojih bratov boš postavil za kralja nad seboj. Nad seboj ne smeš postaviti tujca, ki ni tvoj brat.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Toda ta si ne bo množil konj niti ljudstvu ne bo povzročil, da se vrne v Egipt, z namenom, da bi množil konje, ker kakor ti je Gospod rekel: ›Odslej se ne boš več vrnil po tisti poti.‹
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Niti si k sebi ne bo množil žená, da njegovega srca ne odvrnejo stran niti k sebi ne bo silno pomnožil srebra in zlata.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 In zgodilo se bo, ko sedi na prestolu svojega kraljestva, da si bo zapisal prepis te postave v knjigo iz te, ki je pred duhovniki Lévijevci,
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 in ta bo z njim in iz nje bo bral vse dni svojega življenja, da se bo lahko učil bati se Gospoda, svojega Boga, da ohranja vse besede te postave in te zakone, da jih izvršuje,
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 da njegovo srce ne bo povzdignjeno nad njegove brate in da se ne obrne proč od zapovedi, k desni roki ali k levi, z namenom, da lahko podaljša svoje dni v svojem kraljestvu, on in njegovi otroci, v sredi Izraela.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.