< Apostolska dela 6 >
1 In v tistih dneh, ko je bilo število učencev pomnoženo, je nastalo mrmranje Grkov zoper Hebrejce, ker so bile njihove vdove zapostavljene pri vsakodnevni oskrbi.
A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum.
2 Potem je dvanajsterica k sebi poklicala množico učencev in rekla: »To ni razlog, da bi opuščali Božjo besedo in stregli [pri] mizah.
Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba.
3 Zatorej bratje, poiščite med seboj sedem mož, na dobrem glasu, polnih Svetega Duha in modrosti, ki jim lahko določimo to opravilo.
’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki
4 Toda mi se bomo predali v nenehno molitev in službo besede.«
mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”
5 In ta beseda je ugajala vsej množici. In izbrali so Štefana, moža, polnega vere in Svetega Duha in Filipa in Prohorja in Nikánorja in Timona in Parmenája ter Nikolaja, spreobrnjenca iz Antiohije,
Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci.
6 ki jih so postavili pred apostole. In ko so molili, so nanje položili svoje roke.
Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.
7 In Božja beseda je rasla in število učencev v Jeruzalemu se je silno pomnožilo in velika skupina duhovnikov je bila pokorna veri.
Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.
8 In Štefan je, poln vere in moči, delal med ljudmi velike čudeže in čudežne moči.
To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane.
9 Potem so vstali nekateri iz sinagoge, ki se je imenovala sinagoga Libertincev in Cirencev in Aleksandríncev in teh iz Kilikije ter iz Azije in so razpravljali s Štefanom.
Sai hamayya ta taso daga’yan ƙungiyar Majami’a na’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
10 Niso pa se mogli upirati modrosti in duhu, po katerem je govoril.
amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.
11 Tedaj so podkupili može, ki so rekli: »Slišali smo ga govoriti bogokletne besede zoper Mojzesa in zoper Boga.«
Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”
12 In razvneli so ljudi in starešine ter pisarje in prišli nad njega in ga zgrabili ter ga privedli k vélikemu zboru
Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa.
13 in postavili krive priče, ki so rekle: »Ta človek ne preneha govoriti bogokletnih besed proti temu svetemu prostoru in postavi,
Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka.
14 kajti slišali smo ga govoriti, da bo ta Jezus Nazarečan uničil ta kraj in spremenil običaje, ki nam jih je izročil Mojzes.«
Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”
15 In vsi, ki so sedeli v vélikem zboru, so neomajno zrli vanj in videli njegov obraz, kot bi bil obraz angela.
Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.