< Apostolska dela 14 >
1 Pripetilo pa se je v Ikóniju, da sta oba skupaj odšla v judovsko sinagogo in tako govorila, da je velika množica, tako Judov kakor tudi Grkov, verovala.
A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
2 Toda neverni Judje so razvneli pogane in hudobno vplivali na njihovo mišljenje proti bratom.
Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
3 Ostala sta torej dolgo časa in pogumno govorila v Gospodu, ki je dal pričevanje k besedi svoje milosti in zagotovil, da so se po njunih rokah dogajala znamenja in čudeži.
Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
4 Vendar je bila množica iz mesta razdeljena; del je držal z Judi, del pa z apostoli.
Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5 In ko je bil storjen napad, ki so ga sprožili tako pogani kakor tudi Judje s svojimi vladarji, da z njima kruto ravnajo in da ju kamnajo,
Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
6 sta bila o tem obveščena in pobegnila v Listro in Derbo, mesti v Likaoniji in k področju, ki leži naokoli
da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
7 in tam oznanjala evangelij.
a can suka yi wa'azin bishara.
8 In v Listri je sedel nek mož, nemočen v svojih stopalih, pohabljen že od maternice svoje matere, ki nikoli ni hodil.
A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
9 Isti je slišal Pavla govoriti. Ta je neomajno zrl vanj in zaznavajoč, da je imel vero, da bi bil ozdravljen,
Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
10 je z močnim glasom rekel: »Stopi pokonci na svoja stopala.« In poskočil je in hodil.
Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11 In ko je množica videla, kaj je Pavel storil, so povzdignili svoje glasove, rekoč v likaonskem jeziku: »K nam dol sta prišla bogova v človeški podobi.«
Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
12 In Barnaba so imenovali Jupitra, Pavla pa Merkurja, ker je bil glavni govornik.
Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
13 Potem je Jupitrov svečenik, ki je bil pred njihovim mestom, k velikim vratom privedel vola in vence in z množico želel opraviti žrtvovanje.
Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14 Nakar, ko sta apostola Barnaba in Pavel to slišala, sta razparala svoja oblačila in stekla med množico, vzklikajoč
Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
15 in govoreč: »Možje, zakaj počnete te stvari? Tudi midva sva z vami človeka podobnih strasti in oznanjava vam, da naj bi se od teh ničevosti obrnili k živemu Bogu, ki je naredil nebo in zemljo in morje ter vse stvari, ki so v njih,
Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
16 ki je v prejšnjih časih prenašal vse narode, da hodijo po svojih lastnih poteh.
A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17 Vendar sebe ni pustil brez pričevanja, ker je delal dobro in nam dajal dež z neba ter rodovitna obdobja in naša srca napolnjeval s hrano in veseljem.«
Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
18 In s temi besedami sta komaj zadržala množico, da jima ni opravila žrtvovanja.
Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19 In tja so prišli neki Judje iz Antiohije in Ikónija, ki so pregovorili množico in ko so kamnali Pavla, so ga izvlekli iz mesta, ker so mislili, da je bil mrtev.
Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
20 Vendar ko so ga obkrožili učenci, je vstal ter prišel v mesto in naslednji dan z Barnabom odšel v Derbo.
Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21 In ko sta temu mestu oznanila evangelij ter mnoge učila, sta se ponovno vrnila v Listro in v Ikónij in Antiohijo
Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
22 ter krepila duše učencev in jih spodbujala, naj nadaljujejo v veri in da moramo skozi veliko stisko vstopiti v Božje kraljestvo.
Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
23 In ko sta jim v vsaki cerkvi odredila starešine ter molila s postom, sta jih priporočila Gospodu, ki so mu verovali.
Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
24 In potem, ko sta prepotovala skozi vso Pizidijo, sta prišla v Pamfilijo.
Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
25 In ko sta besedo oznanila v Pergi, sta odšla dol v Atálejo
Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
26 in od tam sta odjadrala v Antiohijo, od koder sta bila priporočena Božji milosti za delo, ki sta ga izvršila.
Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27 In ko sta prišla in so skupaj zbrali cerkev, sta jim ponovila vse, kar je Bog z njima storil in kako je odprl vrata vere k poganom.
Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
28 In tam sta z učenci ostala dolgo časa.
Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.