< 2 Samuel 14 >

1 Torej Cerújin sin Joáb je zaznal, da je bilo kraljevo srce [nagnjeno] k Absalomu.
Yowab, ɗan Zeruhiya ya gane cewa zuriyar sarki ta koma ga Absalom.
2 Joáb je poslal v Tekóo in od tam privedel modro žensko ter ji rekel: »Prosim te, hlini se, da si žalovalka in sedaj si nadeni žalovalno obleko in se ne mazili z oljem, temveč bodi kakor ženska, ki je dolgo časa žalovala za mrtvim
Saboda haka Yowab ya aiki wani zuwa Tekowa, ya sa a zo da wata mace mai hikima. Ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki. Ki sa rigar makoki, kada kuwa ki shafa mai. Ki yi kamar macen da ta yi kwanaki da yawa, tana makokin matattu.
3 in pojdi h kralju in mu govori na ta način.« Tako je Joáb položil besede v njena usta.
Sa’an nan ki je wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai Yowab ya faɗa mata duk abin da za tă faɗa.
4 Ko je ženska iz Tekóe govorila kralju, je padla na svoj obraz do tal in se globoko priklonila ter rekla: »Pomagaj, oh kralj.«
Da macen da ta fito daga Tekowa ta je wajen sarki, sai ta rusuna har ƙasa don bangirma, sai ta ce, “Ka taimake ni, ya sarki!”
5 Kralj ji je rekel: »Kaj te pesti?« Odgovorila je: »Res sem vdova in moj soprog je mrtev.
Sarki ya ce mata, “Mece ce matsalarki?” Sai ta ce, “Tabbatacce, ni gwauruwa ce; mijina ya mutu.
6 Tvoja pomočnica je imela dva sinova in skupaj sta se prepirala na polju in tam ni bilo nobenega, da ju loči, temveč je eden udaril drugega in ga usmrtil.
Baiwarka tana da’ya’ya maza biyu. Suka yi faɗa da juna a fili, kuma ba wanda yake can don yă raba su. Ɗayan ya bugi ɗayan, ya kashe shi.
7 Glej, celotna družina je vstala zoper tvojo pomočnico in rekli so: ›Izroči tega, ki je usmrtil svojega brata, da ga bomo lahko ubili za življenje njegovega brata, ki ga je usmrtil in tudi dediča bomo uničili.‹ Tako bodo pogasili moj ogorek, ki je ostal in mojemu soprogu ne bodo pustili niti imena niti ostanka na tej zemlji.«
To, ga duk iyali sun hau kan baiwarka, suna cewa, ‘Ki ba mu ɗayan da ya kashe ɗan’uwansa mu kashe don ran ɗan’uwansa da ya kashe; sa’an nan za mu hallaka magājin shi ma.’ Za su kashe garwashin wuta mai ci da nake da shi kaɗai, su bar mijina ba suna, ba jika, a duniya.”
8 Kralj je rekel ženski: »Pojdi k svoji hiši in glede tebe dal bom zadolžitev.«
Sarki ya ce wa macen, “Koma gida, zan ba da umarni a madadinki.”
9 Ženska iz Tekóe je rekla kralju: »Moj gospod, oh kralj, krivičnost bodi na meni in na hiši mojega očeta, kralj in njegov prestol pa naj bosta brez krivde.«
Amma macen da ta fito daga Tekowa ta ce, “Ranka yă daɗe, sarki! Bari alhakin shari’arka yă kasance a kaina da gidan mahaifina, kai sarki da gidan mulkinka, ba ku da laifi a ciki.”
10 Kralj je rekel: »Kdorkoli ti karkoli reče, ga privedi k meni in ne bo se te več dotaknil.«
Sai sarki ya ce, “In wani ya yi miki magana, ki kawo shi wurina, ba zai kuwa ƙara damunki ba.”
11 Potem je rekla: »Prosim te, naj se kralj spomni Gospoda, svojega Boga, da ti nočeš trpeti, da krvni maščevalci še naprej uničujejo, da ne bi uničili mojega sina.« Rekel je: »Kakor Gospod živi niti en las tvojega sina ne bo padel k zemlji.«
Sai ta ce, “To, bari sarki yă rantse da Ubangiji Allahnsa don yă hana mai ramako yin ƙarin hallakawar da aka yi, domin kada a hallaka ɗana.” Sai ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, babu gashi guda na ɗanki da zai fāɗi ƙasa.”
12 Potem je ženska rekla: »Naj tvoja pomočnica, prosim te, spregovori eno besedo mojemu gospodu kralju.« In ta je rekel: »Povej.«
Sai matar ta ce, “Bari baiwarka ta ƙara yin magana sau ɗayan nan wa ranka yă daɗe.” Ya ce, “Ki faɗa.”
13 Ženska je rekla: »Zakaj si potem mislil storiti takšno stvar zoper Božje ljudstvo? Kajti kralj govori to stvar kakor nekdo, ki je pomanjkljiv, v tem, da kralj ne privede ponovno domov svojega pregnanega.
Matar ta ce, “To, don me ka yi wa mutanen Allah irin wannan abu? Sa’ad da sarki ya ce haka, ashe, ba ka hukunta kanka ke nan ba, tun da yake sarki bai yarda ɗansa yă komo gida ba?
14 Kajti mi moramo umreti in smo kakor voda, razlita na tla, ki ne more biti ponovno zbrana niti Bog ne upošteva nobene osebe, vendar snuje način, da njegov pregnani ne bo izključen od njega.
Kamar ruwan da ya zuba a ƙasa, wanda ba a iya kwasa, haka dole mu mutu. Amma Allah ba ya ɗaukan rai; a maimako, yakan ƙirƙiro hanyoyi domin mutumin da aka kora kada yă kasance yasasshe daga gare shi.
15 Zdaj torej, ko sem prišla, da o tej stvari govorim mojemu gospodu kralju, je to zato, ker me je ljudstvo prestrašilo. Tvoja pomočnica je rekla: ›Spregovorila bom torej kralju. Lahko se zgodi, da bo kralj izpolnil zahtevo svoje pomočnice.‹
“Yanzu ga shi na zo don in faɗa wannan wa ranka yă daɗe sarki, don mutane sun tsorata ni. Baiwarka ta yi tunani ta ce, ‘Zan yi magana wa sarki; wataƙila yă yi abin da baiwarsa ta roƙa.
16 Kajti kralj bo slišal, da svojo pomočnico osvobodi iz roke človeka, ki hoče skupaj uničiti tako mene in mojega sina iz Božje dediščine.
Wataƙila sarki zai yarda yă ceci baiwarsa daga hannun mutumin nan da yake ƙoƙari yă hallaka ni da ɗana daga gādon da Allah ya ba mu.’
17 Potem je tvoja pomočnica rekla Gospodu: ›Beseda mojega gospoda kralja bo sedaj tolažilna, kajti kakor angel od Boga, tako je moj gospod kralj, da razlikuje dobro in slabo, zato bo Gospod, tvoj Bog, s teboj.‹«
“Yanzu kuwa baiwarka tana cewa, ‘Bari magana ranka yă daɗe sarki yă ba ni hutu, gama ranka yă daɗe sarki yana kama da mala’ikan Allah cikin rarrabe nagarta da mugunta. Bari Ubangiji Allahnka yă kasance tare da kai.’”
18 Potem je kralj ženski odgovoril in rekel: »Ne skrivaj pred menoj, prosim te, stvari, ki jo bom vprašal.« Ženska je rekla: »Naj moj gospod kralj sedaj spregovori.«
Sai sarki ya ce wa matar, “Kada ki ɓoye mini kome daga abin da zan tambaye ki.” Matar ta ce, “Bari ranka yă daɗe sarki yă yi tambaya.”
19 Kralj je rekel: » Mar ni v vsem tem s teboj Joábova roka?« Ženska je odgovorila ter rekla: » Kakor živi tvoja duša, moj gospod kralj, nihče se ne more izogniti ne na desno ne na levo od tega, kar je moj gospod kralj govoril, kajti tvoj služabnik Joáb mi je zaukazal in on je položil vse te besede v usta tvoje pomočnice,
Sarki ya ce, “Anya, babu hannun Yowab a cikin dukan wannan?” Matar ta ce, “Muddin kana a raye, ranka yă daɗe sarki, ba wanda zai juya dama ko hagu daga wani abin da ranka yă daɗe sarki ya faɗa. I, bawanka Yowab ne ya umarce ni in yi wannan, shi ne kuma ya sa kalmomin nan a bakin baiwarka.
20 da privleče na dan to obliko govora, je tvoj služabnik Joáb storil to stvar. In moj gospod je moder, glede na modrost Božjega angela, da ve vse stvari, ki so na zemlji.«
Bawanka Yowab ne ya yi haka don yă daidaita al’amura. Ranka yă daɗe yana da hikima iri ta mala’ikan Allah, ya san dukan kome da yake faruwa a ƙasar.”
21 Kralj je rekel Joábu: »Glej torej, jaz sem storil to stvar, zato pojdi, ponovno privedi mladeniča Absaloma.«
Sarki ya ce wa Yowab, “To, da kyau, zan yi haka. Je ka, ka dawo da saurayin nan Absalom.”
22 Joáb je padel k tlom, na svoj obraz, se upognil in zahvalil kralju in Joáb je rekel: »Danes tvoj služabnik vé, da sem našel milost v tvojem pogledu, moj gospod, oh kralj, v tem, da je kralj izpolnil zahtevo svojega služabnika.«
Yowab ya rusuna har ƙasa don bangirma, ya kuma yi wa sarki kyakkyawar fata. Yowab ya ce, “Yau, bawanka ya sani ya sami tagomashi a gare ka, ranka yă daɗe sarki, gama sarki ya ji roƙon bawansa.”
23 Tako je Joáb vstal in odšel v Gešur in Absaloma privedel v Jeruzalem.
Sa’an nan Yowab ya tafi Geshur ya dawo da Absalom Urushalima.
24 Kralj je rekel: »Naj se obrne k svoji lastni hiši in naj ne vidi mojega obraza.« Tako se je Absalom vrnil k svoji lastni hiši in ni videl kraljevega obraza.
Amma sarki ya ce, “Yă tafi gidansa; kada yă zo yă gan ni.” Saboda haka Absalom ya tafi gidansa, bai kuwa je ganin sarki ba.
25 Toda v vsem Izraelu ni bilo nikogar, da bi bil tako zelo hvaljen zaradi svoje lepote kakor Absalom. Od podplata svojega stopala, celo do krone njegove glave, ni bilo na njem nobenega madeža.
A cikin dukan Isra’ila babu wanda ake yabon kyansa kamar Absalom. Tun daga kansa har zuwa tafin ƙafansa babu tabo a jikinsa.
26 In ko je ostrigel svojo glavo (kajti ob koncu vsakega leta si jo je ostrigel, ker so bili lasje na njem težki, zato jo je ostrigel) si je stehtal lase svoje glave, dvesto šeklov po kraljevi teži.
A duk sa’ad da ya aske gashin kansa (yakan aske kansa lokaci-lokaci sa’ad da ya yi masa nauyi) yakan auna shi, nauyin gashin kuwa yakan kai wajen shekel ɗari biyu a ma’aunin da ake awo.
27 Absalomu so se tam rodili trije sinovi in ena hči, ki ji je bilo ime Tamara. Bila je ženska lepega obličja.
Aka haifa wa Absalom’ya’ya uku maza da’ya mace guda. Sunanta Tamar, ta kuwa zama kyakkyawan mace ƙwarai.
28 Tako je Absalom dve polni leti prebival v Jeruzalemu in ni videl kraljevega obraza.
Absalom ya zauna a Urushalima shekara biyu amma ba tare da ganin fuskar sarki ba.
29 Zato je Absalom poslal po Joába, da ga pošlje h kralju, toda ta ni hotel priti k njemu in ko je drugič ponovno poslal, ta ni hotel priti.
Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don yă aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Saboda haka ya sāke aika sau na biyu, amma ya ƙi yă zo.
30 Zato je rekel svojim služabnikom: »Glejte, Joábovo polje je v bližini mojega in tam ima ječmen. Pojdite in ga požgite.« In Absalomovi služabniki so zažgali polje.
Sai ya ce wa bayinsa, “Duba, gonar Yowab tana gab da tawa, kuma yana da sha’ir a can. Ku je ku sa mata wuta.” Sai bayin Absalom suka sa wa gonar wuta.
31 Potem je Joáb vstal in prišel k Absalomu v njegovo hišo ter mu rekel: »Zakaj so tvoji služabniki zažgali moje polje?«
Sa’an nan Yowab ya tafi gidan Absalom ya ce masa, “Me ya sa bayinka suka sa wa gonata wuta?”
32 Absalom je odgovoril Joábu: »Glej, poslal sem k tebi, rekoč: ›Pridi sèm, da te lahko pošljem h kralju, da rečem: ›Zakaj sem prišel iz Gešurja?‹‹ Zame bi bilo dobro, da bi bil še vedno tam. Sedaj mi torej pusti videti kraljev obraz in če bo kakršnakoli krivičnost v meni, naj me ubije.«
Absalom ya ce wa Yowab, “Kai, na aika, ‘Ka zo nan don in aike ka wurin sarki ka tambaya, “Me ya sa na dawo daga Geshur? Ai, ya fi mini a ce ina can har yanzu!”’ Yanzu kuwa, ina so in ga sarki, kuma idan na yi wani laifi, to, yă kashe ni.”
33 Tako je Joáb prišel h kralju in mu povedal in ko je dal poklicati Absaloma, je ta prišel h kralju in se pred kraljem priklonil na svoj obraz do tal in kralj je poljubil Absaloma.
Saboda haka Yowab ya tafi wurin sarki ya gaya masa wannan. Sai sarki ya aika aka zo da Absalom, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki. Sarki kuwa ya sumbaci Absalom.

< 2 Samuel 14 >