< 2 Kralji 15 >

1 V sedemindvajsetem letu Izraelovega kralja Jerobeáma je začel kraljevati Azarjá, sin Judovega kralja Amacjája.
A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Šestnajst let je bil star, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval dvainpetdeset let. Ime njegove matere je bilo Jehólja iz Jeruzalema.
Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
3 Delal je to, kar je bilo pravilno v Gospodovih očeh, glede na vse, kar je delal njegov oče Amacjá,
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
4 razen, da niso bili odstranjeni visoki kraji. Ljudstvo je na visokih krajih še vedno žrtvovalo in zažigalo kadilo.
Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
5 Gospod je udaril kralja, tako da je bil gobavec do dneva svoje smrti in prebival v posebni hiši. Kraljev sin Jotám pa je bil nad hišo in sodil ljudstvu dežele.
Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
6 Ostala Azarjájeva dela in vse, kar je storil, mar niso zapisana v kroniški knjigi Judovih kraljev?
Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
7 Tako je Azarjá zaspal s svojimi očeti in v Davidovem mestu so ga pokopali z njegovimi očeti in namesto njega je zakraljeval njegov sin Jotám.
Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
8 V osemintridesetem letu Judovega kralja Azarjá je Jerobeámov sin Zaharija šest mesecev kraljeval nad Izraelom v Samariji.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
9 Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh, kakor so počeli njegovi očetje. Ni se oddvojil od grehov Nebátovega sina Jerobeáma, ki je Izraela pripravil, da greši.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
10 Jabéšov sin Šalúm se je zoper njega zarotil, ga udaril vpričo ljudstva, ga usmrtil in zakraljeval namesto njega.
Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
11 Ostala Zaharijeva dela, glej, zapisana so v kroniški knjigi Izraelovih kraljev.
Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
12 To je bila beseda od Gospoda, ki jo je govoril Jehúju, rekoč: »Tvoji sinovi bodo sedeli na Izraelovem prestolu do četrtega rodu.« In tako se je zgodilo.
Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
13 Jabéšov sin Šalúm je začel kraljevati v devetintridesetem letu Judovega kralja Uzíjaha, in cel mesec je kraljeval v Samariji.
Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
14 Kajti Gadíjev sin Menahém je iz Tirce odšel gor, prišel v Samarijo in v Samariji udaril Jabéševega sina Šalúma, ga umoril in zakraljeval namesto njega.
Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
15 Ostala Šalúmova dela in njegova zarota, ki jo je storil, glej, zapisana so v kroniški knjigi Izraelovih kraljev.
Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Potem je Menahém udaril Tifsáha in vse, ki so bili v njem in njegove pokrajine od Tirce, ker se niso odprli k njemu, zato ga je udaril, in vse ženske, ki so bile v njem, ki so bile z otrokom, je razparal.
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
17 V devetintridesetem letu Judovega kralja Azarjája je nad Izraelom začel kraljevati Gadíjev sin Menahém in v Samariji je kraljeval deset let.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
18 Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh. Vse svoje dni se ni oddvojil od grehov Nebátovega sina Jerobeáma, ki je Izraela pripravil, da greši.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
19 Zoper deželo je prišel asirski kralj Pul in Menahém je dal Pulu tisoč talentov srebra, da bi bila njegova roka lahko z njim, da potrdi kraljestvo v njegovi roki.
Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
20 Menahém je od Izraela zahteval denar od vseh mogočnih mož obilja, od vsakega moža petdeset šeklov srebra, da jih dá asirskemu kralju. Tako se je kralj Asirije obrnil nazaj in ni ostal v deželi.
Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
21 Ostala Menahémova dela in vse, kar je storil, mar niso zapisana v kroniški knjigi Izraelovih kraljev?
Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
22 Menahém je zaspal s svojimi očeti in namesto njega je zakraljeval njegov sin Pekahjá.
Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
23 V petdesetem letu Judovega kralja Azarjája je nad Izraelom v Samariji začel kraljevati Menahémov sin Pekahjá in kraljeval je dve leti.
A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
24 Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh; ni se oddvojil od grehov Nebátovega sina Jerobeáma, ki je Izraela pripravil, da greši.
Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
25 Toda njegov poveljnik, Remaljájev sin Pékah, se je zarotil zoper njega in ga udaril v Samariji, v palači kraljeve hiše z Argóbom in Arjéjem in z njim petdeset mož izmed Gileádcev, ga ubil in zakraljeval namesto njega.
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
26 Ostala Pekahjájeva dela in vse, kar je storil, glej, ta so zapisana v kroniški knjigi Izraelovih kraljev.
Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
27 V dvainpetdesetem letu Judovega kralja Azarjá je nad Izraelom v Samariji začel kraljevati Remaljájev sin Pékah in kraljeval je dvajset let.
A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
28 Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh. Ni se oddvojil od grehov Nebátovega sina Jerobeáma, ki je Izraela pripravil, da greši.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
29 V dneh Izraelovega kralja Pékaha je prišel asirski kralj Tiglát Piléser in zavzel Ijón, Abél Bet Maáho, Janóah, Kedeš, Hacór, Gileád in Galilejo, vso Neftálijevo deželo in jih ujete odvedel v Asirijo.
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
30 Elájev sin Hošéa se je zarotil zoper Remaljájevega sina Pékaha, ga udaril, usmrtil in namesto njega zakraljeval v dvajsetem letu Uzíjahovega sina Jotáma.
Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
31 Ostala Pékahova dela in vse, kar je storil, glej, ta so zapisana v kroniški knjigi Izraelovih kraljev.
Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 V drugem letu Remaljájevega sina Pékaha, Izraelovega kralja, je začel kraljevati Jotám, sin Judovega kralja Uzíjaha.
A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
33 Petindvajset let je bil star, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval šestnajst let. Ime njegove matere je bilo Jerúša, Cadókova hči.
Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
34 Delal je, kar je bilo pravilno v Gospodovih očeh. Storil je glede na vse, kar je storil njegov oče Uzíjah.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
35 Vendar visoki kraji niso bili odstranjeni. Ljudstvo je še vedno žrtvovalo in na visokih krajih zažigalo kadilo. Zgradil je višja velika vrata Gospodove hiše.
Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
36 Torej preostala izmed Jotámovih dejanj in vse, kar je storil, mar niso zapisana v kroniški knjigi Judovih kraljev?
Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
37 V tistih dneh je Gospod zoper Juda začel pošiljati sirskega kralja Recína in Remaljájevega sina Pékaha.
(A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
38 Jotám je zaspal s svojimi očeti in bil s svojimi očeti pokopan v mestu svojega očeta Davida in namesto njega je zakraljeval njegov sin Aház.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kralji 15 >