< 2 Kroniška 33 >

1 Manáse je bil star dvanajst let, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval petinpetdeset let,
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 toda počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh, podobno ogabnostim poganov, ki jih je Gospod pregnal pred Izraelovimi otroki.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Kajti ponovno je zgradil visoke kraje, ki jih je njegov oče Ezekíja porušil, vzdignil Báalove oltarje, naredil ašere in oboževal vso vojsko neba ter jim služil.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 Prav tako je zgradil oltarje v Gospodovi hiši, o kateri je Gospod rekel: »V Jeruzalemu bo moje ime na veke.«
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 Zgradil je oltarje za vso vojsko neba v dveh dvorih Gospodove hiše.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 Svoje otroke je izročil, da gredo skozi ogenj v dolini sina Hinómovega. Obeleževal je tudi čase, uporabljal izrekanje urokov, uporabljal čarovništvo in postopal z osebnim duhom in s čarovniki. Storil je mnogo zla v Gospodovih očeh, da ga izziva do jeze.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Postavil je izrezljano podobo, malika, ki ga je naredil v Božji hiši, o kateri je Bog rekel Davidu in njegovemu sinu Salomonu: »V tej hiši, v Jeruzalemu, ki sem jo izbral pred vsemi Izraelovimi rodovi, bom svoje ime postavil na veke.
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Niti ne bom več odstranil Izraelovega stopala iz dežele, ki sem jo določil za vaše očete, tako da bodo pazili, da storijo vse, kar sem jim zapovedal, glede na celotno postavo, zakone in odredbe po Mojzesovi roki.
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 Tako je Manáse storil Judu in prebivalcem Jeruzalema, da zaidejo in da počnejo huje kakor pogani, ki jih je Gospod uničil pred Izraelovimi otroki.
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Gospod je spregovoril Manáseju in njegovemu ljudstvu, toda niso hoteli prisluhniti.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 Zato je Gospod nadnje privedel poveljnike vojske asirskega kralja, ki so Manáseja zajeli med trnjem in ga zvezali z okovi ter ga odvedli v Babilon.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 Ko je bil v stiski, je iskal Gospoda, svojega Boga in se silno ponižal pred Bogom svojih očetov
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 in molil k njemu in izprošen je bil od njega in slišal je njegovo ponižno prošnjo in ga ponovno privedel k Jeruzalemu, v njegovo kraljestvo. Potem je Manáse spoznal, da je bil Gospod Bog.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 Torej po tem je zgradil zid zunaj Davidovega mesta, na zahodni strani Gihona, v dolini, celo pri vhodu velikih ribjih vrat in obdal Ofel ter ga dvignil na zelo veliko višino in vojne poveljnike postavil v vsa utrjena Judova mesta.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 Odstranil je tuje bogove in malike iz Gospodove hiše in vse oltarje, ki jih je zgradil na gori Gospodove hiše in v Jeruzalemu ter jih vrgel iz mesta.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 Popravil je Gospodov oltar in na njem žrtvoval mirovne daritve in zahvalne daritve in Judu zapovedal, da služi Gospodu, Izraelovemu Bogu.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 Kljub temu je ljudstvo še vedno darovalo na visokih krajih, vendar samo Gospodu, svojemu Bogu.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 Torej preostala izmed Manásejevih dejanj, njegova molitev k njegovemu Bogu in besede vidcev, ki so mu govorili v imenu Gospoda, Izraelovega Boga, glej, ta so zapisana v knjigi Izraelovih kraljev.
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 Tudi njegova molitev in kako je bil Bog izprošen od njega, ves njegov greh, njegov prekršek in kraji, na katerih si je zgradil visoke kraje ter postavil ašere in rezane podobe, preden je bil ponižan. Glej, ta so zapisana med izreki vidcev.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Tako je Manáse zaspal s svojimi očeti in pokopali so ga v njegovi lastni hiši. Namesto njega je zakraljeval njegov sin Amón.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amón je bil star dvaindvajset let, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval dve leti.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 Toda počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh, kakor je počel njegov oče Manáse, kajti Amón je žrtvoval vsem izrezljanim podobam, ki jih je naredil njegov oče Manáse in jim služil.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 Ni se ponižal pred Gospodom, kakor se je ponižal njegov oče Manáse, temveč je Amón bolj in bolj grešil.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 In njegovi služabniki so se zarotili zoper njega in ga usmrtili v njegovi lastni hiši.
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 Toda ljudstvo dežele je usmrtilo vse tiste, ki so se zarotili zoper kralja Amóna in ljudstvo dežele je postavilo njegovega sina Jošíja za kralja namesto njega.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.

< 2 Kroniška 33 >