< 2 Kroniška 12 >
1 Pripetilo se je, ko je Rehabám utrdil kraljestvo in se okrepil, da je zapustil Gospodovo postavo in ves Izrael z njim.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 Pripetilo se je, da je v petem letu kralja Rehabáma egiptovski kralj Šišák prišel gor zoper Jeruzalem, ker so se pregrešili zoper Gospoda,
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 s tisoč dvesto bojnimi vozovi in šestdeset tisoč konjeniki. Ljudstva, ki so prišli z njim iz Egipta, je bilo brez števila: Libijci, Súkijci in Etiopci.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 Zavzel je utrjena mesta, ki pripadajo Judu in prišel do Jeruzalema.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Potem je prišel prerok Šemajá k Rehabámu in k Judovim princem, ki so bili zaradi Šišáka zbrani skupaj v Jeruzalemu ter jim rekel: ›Tako govori Gospod: ›Vi ste zapustili mene in zato sem tudi jaz vas prepustil v Šišákovo roko.‹«
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Nakar so se Izraelovi princi in kralj ponižali ter rekli: » Gospod je pravičen.«
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 Ko je Gospod videl, da so se ponižali, je beseda od Gospoda prišla k Šemajáju, rekoč: »Oni so se ponižali, zato jih ne bom uničil, temveč jim bom zagotovil nekaj osvoboditve, in moj bes ne bo izlit na Jeruzalem po Šišákovi roki.
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 Kljub temu bodo njegovi služabniki, da bodo lahko spoznali moje služenje in služenje kraljestvom dežel.«
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 Tako je egiptovski kralj Šišák prišel gor nad Jeruzalem in odnesel zaklade Gospodove hiše in zaklade kraljeve hiše. Vse je vzel. Odnesel je tudi ščite iz zlata, ki jih je naredil Salomon.
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 Namesto teh je kralj Rehabám naredil ščite iz brona in jih predal v roke poveljnika straže, ki je varoval vhod kraljeve hiše.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 Ko je kralj vstopil v Gospodovo hišo, je prišla straža ter jih nosila in jih [potem] ponovno prinesla v stražarnico.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Ko se je ponižal, se je Gospodov bes odvrnil od njega, da ga ne bi povsem uničil. Tudi v Judu so stvari šle dobro.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 Tako se je kralj Rehabám okrepil v Jeruzalemu in kraljeval, kajti Rehabám je bil star enainštirideset let, ko je začel kraljevati in sedemnajst let je kraljeval v Jeruzalemu, mestu, ki ga je Gospod izbral izmed vseh Izraelovih rodov, da tam postavi svoje ime. Ime njegove matere je bilo Naáma, Amónka.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Počel je zlo, ker svojega srca ni pripravil, da išče Gospoda.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 Torej dejanja Rehabáma, prva in zadnja, mar niso zapisana v knjigi preroka Šemajája in vidca Idója glede rodovnikov? In nenehno so bile vojne med Rehabámom in Jerobeámom.
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 Rehabám je zaspal s svojimi očeti in pokopan je bil v Davidovem mestu. Namesto njega je zakraljeval njegov sin Abíja.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.