< 1 Samuel 3 >

1 Otrok Samuel pa je pred Élijem služil Gospodu. V tistih dneh je bila Gospodova beseda dragocena; ni bilo odprtega videnja.
Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
2 Pripetilo se je ob tistem času, ko se je Éli ulegel na svojem mestu in so njegove oči začenjale temneti, da ni mogel videti.
Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
3 Preden se je ugasnila Božja svetilka v Gospodovem templju, kjer je bila Božja skrinja in se je Samuel ulegel k spanju,
Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
4 je Gospod poklical Samuela in ta je odgovoril: »Tukaj sem.«
Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 Stekel je k Éliju in rekel: »Tukaj sem, kajti klical si me.« Ta pa je rekel: »Nisem klical, ponovno se ulezi.« In odšel je in se ulegel.
Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
6 Gospod je ponovno poklical: »Samuel.« Samuel je vstal in odšel k Éliju ter rekel: »Tukaj sem, kajti klical si me.« Ta je odgovoril: »Nisem klical, moj sin, ponovno se ulezi.«
Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
7 Torej Samuel še ni poznal Gospoda niti mu Gospodova beseda še ni bila razodeta.
Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
8 Gospod je ponovno, tretjič, poklical Samuela. Ta je vstal, šel k Éliju in rekel: »Tukaj sem, kajti klical si me.« In Éli je zaznal, da je otroka klical Gospod.
Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
9 Zato je Éli rekel Samuelu: »Pojdi, ulezi se in zgodilo se bo, če te pokliče, da boš rekel: ›Govori, Gospod, kajti tvoj služabnik posluša.‹« Tako je Samuel odšel in se ulegel na svojem mestu.
Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
10 Gospod je prišel in obstal ter poklical kakor ob drugih časih: »Samuel, Samuel.« Potem je Samuel odgovoril: »Govori; kajti tvoj služabnik posluša.«
Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
11 Gospod je rekel Samuelu: »Glej, storil bom stvar v Izraelu, ob kateri bo v obeh ušesih vsakega, ki to sliši, zvenelo.
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
12 Na tisti dan bom zoper Élija izpolnil vse stvari, ki sem jih govoril glede njegove hiše. Ko pričnem, bom naredil tudi konec.
A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
13 Kajti povedal sem mu, da bom na veke sodil njegovo hišo zaradi krivičnosti, ki jo on vé, ker sta se njegova sinova naredila nizkotna, on pa jima ni preprečil.
Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
14 Zato sem prisegel Élijevi hiši, da krivičnost Élijeve hiše na veke ne bo očiščena niti s klavno daritvijo niti z darovanjem.«
Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
15 Samuel je ležal do jutra in odprl vrata Gospodove hiše. Samuel pa se je Éliju bal razodeti videnje.
Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
16 Potem je Éli poklical Samuela in rekel: »Samuel, moj sin.« Ta je odgovoril: »Tukaj sem.«
amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
17 Rekel je: »Kaj je stvar, ki ti jo je Gospod povedal? Prosim te, da mi je ne prikriješ. Bog naj ti tako stori in tudi več, če pred menoj skriješ katerokoli stvar od vseh stvari, ki ti jih je povedal.«
Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
18 Samuel mu je povedal vsak delček in ničesar ni skril pred njim. On pa je rekel: »To je Gospod. Naj stori, kar se mu zdi dobro.«
Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
19 Samuel je rasel in Gospod je bil z njim in nobene izmed njegovih besed ni pustil pasti na tla.
Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
20 Ves Izrael, od Dana, celo do Beeršébe, je vedel, da je bil Samuel utrjen, da bi bil Gospodov prerok.
Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
21 Gospod se je ponovno prikazoval v Šilu, kajti Gospod se je v Šilu razodeval Samuelu po Gospodovi besedi.
Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.

< 1 Samuel 3 >