< 1 Samuel 28 >
1 Pripetilo se je v tistih dneh, da so Filistejci zbrali skupaj svojo vojsko za bojevanje, da se borijo z Izraelom. In Ahíš je rekel Davidu: »Zagotovo vedi, da boš šel z menoj ven v bitko, ti in tvoji možje.«
Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
2 David je rekel Ahíšu: »Zagotovo boš vedel, kaj lahko tvoj služabnik stori.« Ahíš je rekel Davidu: »Zato te bom na veke naredil za varuha svoje glave.«
Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
3 Torej Samuel je bil mrtev in ves Izrael ga je objokoval in pokopali so ga v Rami, celo v njegovem lastnem mestu. In Savel je iz dežele odstranil tiste, ki so imeli osebne duhove in čarovnike.
Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
4 Filistejci so se zbrali skupaj in prišli ter se utaborili v Šunému, in Savel je zbral skupaj ves Izrael in utaborili so se v Gilbói.
Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
5 Ko je Savel videl vojsko Filistejcev, je bil prestrašen in njegovo srce je silno trepetalo.
Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
6 Ko je Savel poizvedel od Gospoda, mu Gospod ni odgovoril, niti po sanjah, niti po urimu, niti po prerokih.
Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
7 Potem je Savel rekel svojim služabnikom: »Poiščite mi žensko, ki ima osebnega duha, da lahko grem k njej in jo povprašam.« Njegov služabnik mu je rekel: »Glej, v En Doru je ženska, ki ima osebnega duha.«
Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
8 Savel se je preoblekel in si nadel drugo oblačilo in odšel ter dva moža z njim in ponoči so prišli k ženski. Rekel je: »Prosim te, vedežuj mi po osebnem duhu in katerega ti bom imenoval, mi ga privedi gor.«
Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
9 Ženska mu je rekla: »Glej, ti veš, kaj je storil Savel, kako je iz dežele iztrebil tiste, ki imajo osebne duhove in čarovnike. Zakaj mi potem polagaš zanko za moje življenje, da mi povzročiš, da umrem?«
Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
10 Savel ji je prisegel pri Gospodu, rekoč: » Kakor živi Gospod, se ti za to stvar ne bo pripetila nobena kazen.«
Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
11 Potem je ženska rekla: »Koga naj privedem k tebi?« Rekel je: »Privedi mi gor Samuela.«
Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
12 Ko je ženska zagledala Samuela, je zavpila z močnim glasom. Ženska je spregovorila Savlu, rekoč: »Zakaj si me zavedel? Kajti ti si Savel.«
Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
13 Kralj ji je rekel: »Ne boj se, kajti kaj si videla?« Ženska je rekla Savlu: »Videla sem bogove vzpenjati se iz zemlje.«
Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
14 Rekel ji je: »Kakšne oblike je?« Rekla je: »Starec prihaja gor in pokrit je z ogrinjalom.« Savel je zaznal, da je bil to Samuel in se s svojim obrazom sklonil do tal in se priklonil.
Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
15 Samuel je rekel Savlu: »Zakaj si me vznemiril, da me privedeš gor?« Savel je odgovoril: »Zelo sem zaskrbljen, kajti Filistejci se bojujejo zoper mene, Bog pa je odšel od mene in mi nič več ne odgovarja niti po prerokih niti po sanjah. Zato sem te poklical, da mi lahko daš vedeti, kaj naj storim.«
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
16 Potem je Samuel rekel: »Zakaj potem sprašuješ mene, glede na to, da je Gospod odšel od tebe in je postal tvoj sovražnik?
Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
17 Gospod mu je storil, kakor je govoril po meni, kajti Gospod je iztrgal kraljestvo iz tvoje roke in ga dal tvojemu bližnjemu, torej Davidu,
Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
18 ker ne ubogaš Gospodovega glasu niti ne izvršuješ njegovega krutega besa nad Amálekom, zato ti je Gospod ta dan storil to stvar.
Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
19 Poleg tega bo Gospod tudi Izrael s teboj izročil v roko Filistejcev. Jutri boste ti in tvoji sinovi z menoj. Tudi izraelsko vojsko bo Gospod izročil v roko Filistejcev.«
Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
20 Potem je Savel takoj padel po vsej dolžini na zemljo in bil je boleče prestrašen zaradi Samuelovih besed in v njem ni bilo moči, kajti ves dan ni jedel kruha niti vso noč.
Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
21 Ženska je prišla k Savlu in videla, da je bil silno vznemirjen in mu rekla: »Glej, tvoja pomočnica je ubogala tvoj glas in svoje življenje sem položila v svojo roko in prisluhnila tvojim besedam, ki si mi jih spregovoril.
Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
22 Zdaj torej, prosim te, tudi ti prisluhni glasu svoje pomočnice in naj predte postavim grižljaj kruha in jej, da boš lahko imel moč, ko greš na svojo pot.«
To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
23 Vendar je odklonil in rekel: »Ne bom jedel.« Toda njegovi služabniki so ga, skupaj z žensko, primorali in prisluhnil je njihovemu glasu. Tako je vstal iz tal in sedel na posteljo.
Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
24 Ženska je imela v hiši rejeno tele. Pohitela je, ga zaklala, vzela moko in jo zgnetla ter iz nje spekla nekvašen kruh.
Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
25 In to je prinesla pred Savla in pred njegove služabnike in ti so jedli. Potem so vstali in tisto noč odšli proč.
Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.