< 1 Samuel 14 >
1 Pripetilo se je torej na dan, ko je Savlov sin Jonatan rekel mladeniču, ki je nosil njegovo bojno opremo: »Pridi in pojdiva preko, k filistejski garniziji, ki je na drugi strani.« Toda ni povedal svojemu očetu.
Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
2 Savel je sedel na najbolj oddaljenem delu Gíbee, pod granatovcem, ki je v Migrónu in ljudstva, ki je bilo z njim, je bilo približno šeststo mož.
Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
3 Ahíja, sin Ahitúba, Ikabódov brat, sinú Pinhása, sinú Élija, Gospodovega duhovnika v Šilu, je nosil efód. Ljudstvo pa ni vedelo, da je Jonatan odšel.
A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
4 Med prehodi, ob katerih je Jonatan iskal, da bi šel preko k filistejski garniziji, je bila ostra skala na eni strani in ostra skala na drugi strani. Ime ene je bilo Bocéc, ime druge pa Sene.
A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
5 Sprednji del ene je bil obrnjen proti severu, nasproti Mihmášu in druge proti jugu, nasproti Gíbei.
Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
6 Jonatan je rekel mladeniču, ki je nosil njegovo bojno opremo: »Pridi in pojdiva preko, h garniziji teh neobrezancev. Morda bo Gospod delal za naju, kajti ni omejitve Gospodu, da reši po mnogih ali po peščici.«
Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
7 Njegov nosilec bojne opreme mu je rekel: »Stori vse, kar je v tvojem srcu. Obrni se, glej, jaz sem s teboj glede na tvoje srce.«
Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
8 Potem je Jonatan rekel: »Glej, šla bova preko, k tem možem in se jim bova odkrila.
Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
9 Če nama rečejo: ›Ostanita, dokler ne pridemo do vaju, ‹ potem bova mirno stala na svojem kraju in ne bova šla gor k njim.
In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
10 Toda če rečejo tako: ›Pridita gor k nam, ‹ potem bova šla gor, kajti Gospod jih je izročil v najino roko in to nama bo za znamenje.«
Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
11 Oba izmed njiju sta se odkrila garniziji Filistejcev. Filistejci so rekli: »Poglejte, Hebrejci prihajajo iz lukenj, kamor so se skrili.«
Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
12 Možje iz garnizije so Jonatanu in njegovemu nosilcu bojne opreme odgovorili ter rekli: »Pridita gor k nam in pokazali vama bomo stvar.« Jonatan je rekel svojemu nosilcu bojne opreme: »Pridi gor za menoj, kajti Gospod jih je izročil v Izraelovo roko.«
Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
13 Jonatan je plezal gor po svojih rokah in po svojih stopalih in njegov nosilec bojne opreme za njim in padali so pred Jonatanom. Njegov nosilec bojne opreme pa jih je pobijal za njim.
Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
14 Ta prvi pokol, ki sta ga naredila Jonatan in njegov nosilec bojne opreme, je zajel okrog dvajset mož, kakor bi bilo znotraj pol orala dežele, ki bi jo lahko preoral jarem volov.
A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
15 V vojski na polju in med vsem ljudstvom je bilo trepetanje. Garnizija in plenilci, tudi oni so trepetali in zemlja se je tresla. Tako je bilo zelo veliko trepetanje.
Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
16 Savlovi stražarji v Benjaminovi Gíbei so pogledali in glej, množica se je razblinila in nadaljevali so s podiranjem drug drugega.
Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
17 Potem je Savel rekel ljudstvu, ki je bilo z njim: »Preštejte torej in poglejte, kdo je odšel od nas.« Ko so prešteli, glej, Jonatan in njegov nosilec bojne opreme nista bila tam.
Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
18 Savel je rekel Ahíju: »Prinesi sèm Božjo skrinjo.« Kajti Božja skrinja je bila ob tistem času z Izraelovimi otroki.
Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
19 Pripetilo se je, medtem ko je Savel govoril z duhovnikom, da se je hrup, ki je bil v vojski Filistejcev, nadaljeval in naraščal in Savel je rekel duhovniku: »Umakni svojo roko.«
Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
20 Savel ter vse ljudstvo, ki je bilo z njim, so se zbrali skupaj in prišli k bitki. Glej, meč vsakega moža je bil proti njegovemu tovarišu in tam je bila zelo velika zmeda.
Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
21 Pa tudi Hebrejci, ki so bili pred tem časom s Filistejci, ki so iz okoliške dežele odšli z njimi gor v tabor, celo ti so se prav tako obrnili, da bi bili z Izraelci, ki so bili s Savlom in Jonatanom.
Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
22 Podobno so tudi vsi Izraelovi možje, ki so se skrili na gori Efrájim, ko so slišali, da so Filistejci zbežali, celo oni so sledili tik za njimi v bitko.
Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
23 Tako je Gospod tisti dan rešil Izraela. Bitka je prešla preko k Bet Avenu.
Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
24 Izraelovi možje so bili ta dan užaloščeni, kajti Savel je ljudstvo zaprisegel, rekoč: »Preklet naj bo mož, ki poje kakršnokoli hrano do večera, da bom lahko maščevan na svojih sovražnikih.« Tako nihče izmed ljudstva ni pokusil nobene hrane.
A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
25 Vsi tisti iz dežele so prišli do gozda in tam je bil na tleh med.
Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
26 Ko je ljudstvo prišlo v gozd, glej, je kapljal med, toda noben mož ni iztegnil svoje roke k svojim ustom, kajti ljudstvo se je balo prisege.
Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
27 Toda Jonatan ni slišal, ko je njegov oče ljudstvo obremenil s prisego. Zato je iztegnil konec palice, ki je bila v njegovi roki in jo omočil v satovju in svojo roko nesel k ustom in njegove oči so bile razsvetljene.
Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
28 Potem je odgovoril eden izmed ljudstva in rekel: »Tvoj oče je s prisego strogo obremenil ljudstvo, rekoč: ›Preklet bodi človek, ki danes poje kakršnokoli hrano.‹« In ljudstvo je bilo slabotno.
Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
29 Potem je Jonatan rekel: »Moj oče je vznemiril deželo. Poglej, prosim te, kako so bile moje oči razsvetljene, ker sem okusil malo od tega medu.
Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
30 Kako mnogo bolj, če bi morda ljudstvo danes prosto jedlo od plena svojih sovražnikov, ki so ga našli? Kajti ali ne bi bil sedaj veliko večji pokol med Filistejci?«
Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
31 Ta dan so udarili Filistejce od Mihmáša do Ajalóna, ljudstvo pa je bilo zelo slabotno.
A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
32 In ljudstvo se je vrglo na plen in vzelo ovce, vole in teleta in zaklali so jih na tleh. Ljudstvo jih je jedlo s krvjo.
Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
33 Potem so povedali Savlu, rekoč: »Glej, ljudstvo greši zoper Gospoda v tem, da jedo s krvjo.« Rekel je: »Pregrešili ste se. Zavalite k meni ta dan velik kamen.«
Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
34 Savel je rekel: »Razpršite se med ljudstvo in jim recite: ›Privedite mi sèm vsak človek svojega vola in vsak človek svojo ovco in zakoljite jih tukaj in jejte in ne grešite zoper Gospoda, v tem, da bi jedli s krvjo.‹« Vse ljudstvo je to noč privedlo, vsak človek svojega vola s seboj in so jih tam zaklali.
Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
35 Savel je zgradil oltar Gospodu. Ta isti je bil prvi oltar, ki ga je zgradil Gospodu.
Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
36 Savel je rekel: »Pojdimo ponoči dol za Filistejci in jih plenimo do jutranje svetlobe in ne pustimo nobenega moža od njih.« Rekli so: »Stôri, karkoli se ti zdi dobro.« Potem je rekel duhovniku: »Približajmo se sèm k Bogu.«
Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
37 Savel je vprašal za nasvet od Boga: »Ali naj grem dol za Filistejci? Ali jih boš izročil v Izraelovo roko?« Toda tisti dan mu ni odgovoril.
Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
38 Savel je rekel: »Približajte se sèm, vsi vodje ljudstva in vedite in poglejte, v čem je bil ta greh ta dan.
Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
39 Kajti kakor živi Gospod, ki rešuje Izrael, čeprav bi bil ta na mojem sinu Jonatanu, bo on zagotovo umrl.« Toda tam ni bilo moža izmed ljudstva, da bi mu odgovoril.
Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
40 Potem je vsemu Izraelu rekel: »Vi bodite na eni strani, jaz in moj sin Jonatan pa bova na drugi strani.« Ljudstvo je Savlu reklo: »Stori, kar se ti zdi dobro.«
Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
41 Zato je Savel rekel Gospodu, Izraelovemu Bogu: »Daj popoln žreb.« Zajeta sta bila Savel in Jonatan, toda ljudstvo je bilo izločeno.
Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
42 Savel je rekel: »Vrzite žrebe med menoj in mojim sinom Jonatanom.« In izbran je bil Jonatan.
Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
43 Potem je Savel rekel Jonatanu: »Povej mi kaj si storil.« Jonatan mu je povedal in rekel: »Samo pokusil sem malo medu s koncem palice, ki je bila v moji roki in glej, moram umreti.«
Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
44 Savel je odgovoril: »Bog stori tako in še več, kajti zagotovo boš umrl, Jonatan.«
Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
45 Ljudstvo pa je reklo Savlu: »Ali naj Jonatan umre, ki je izvršil to veliko rešitev duš v Izraelu? Bog ne daj. Kakor Gospod živi, ne bo niti en las iz njegove glave padel na tla, kajti ta dan je delal z Bogom.« Tako je ljudstvo rešilo Jonatana, da ni umrl.
Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
46 Potem je Savel odšel gor od sledenja Filistejcem in Filistejci so odšli k svojemu lastnemu kraju.
Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
47 Tako je Savel vzel kraljestvo nad Izraelom in se boril zoper vse svoje sovražnike na vsaki strani, zoper Moáb, zoper Amónove otroke, zoper Edóm, zoper kralje Cobe in zoper Filistejce in h komurkoli se je obrnil, jim je povzročal skrbi.
Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
48 Zbral je vojsko, udaril Amalečane in Izraela osvobodil iz rok tistih, ki so jih plenili.
Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
49 Torej Savlovi sinovi so bili Jonatan, Jišví in Malkišúa. Imena njegovih dveh hčera sta bili: ime prvorojene Merába in ime mlajše Mihála.
’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
50 Ime Savlove žene je bilo Ahinóam, Ahimáacova hči. Ime poveljnika njegove vojske je bilo Abnêr, sin Savlovega strica Nera.
Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
51 Kiš je bil Savlov oče in Abnêrjev oče Ner je bil Abiélov sin.
Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
52 In tam je bila silna vojna zoper Filistejce vse Savlove dni in ko je Savel zagledal kateregakoli močnega moža ali kateregakoli hrabrega moža, ga je vzel k sebi.
Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.